ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mece Ce Aniyar Shugaban Amurka Game Da Kafa “Tawagar Zaman Lafiya”?

by Sulaiman
5 months ago
Amurka

A ’yan kwanakin nan yayin wani taron manema labarai da ya gudana a fadar White House ta Amurka, shugaban kasar Donald Trump ya ayyana kaddamar da wata kungiya, wadda ya yiwa lakabi da “Tawagar Zaman Lafiya ko “Board of Peace”, wadda za ta gudana a karkashin ikonsa, kuma wadda membobinta za su yiwa gidauniya ta zunzurutun kudi har dala biliyan daya.

A wannan gaba da labarin kaddamar da gidauniyar ke kara bazuwa, har ma wasu kasashe kalilan suka fara nuna amincewa da ita, a daya hannun shugaba Trump ya umarci a janye Amurka daga hukumomin kasa da kasa har 66, ya kuma sake sanar da ficewar kasar ta Amurka daga hukumar lafiya ta duniya WHO a hukumance.

Masharhanta na ganin idan har shugaban na Amurka zai dauki wannan mataki na janye kasarsa daga tarin hukumomin kasa da kasa a dan kankanen lokaci ba tare da wani dalili kwakkwara ba, to mene ne ma’anar kafa wata tafiya mai lakabin “Tawagar Zaman Lafiya”? Amsar hakan a bayyane take, shugaba Trump na yunkurin kara karkata manufofin waje na kasarsa ne zuwa tafarkin amfani da karfin fada-a-ji na bangare daya. Wanda ko shakka babu zai haifarwa Amurka karin kebe kanta maimakon bunkasa cudanya, da kara raba tafiyarta da sauran sassan kasa da kasa.

ADVERTISEMENT

Ko da yake gwamnatin shugaba Trump na cewa, makasudin kafa wannan tafiya ta “Tawagar Zaman Lafiya ko “Board of Peace”, shi ne ingiza matakan wanzar da zaman lafiya, da sake gina wurare da yaki da daidaita ciki har da zirin Gaza, ta amfani da basirar dukkanin sassan kasa da kasa. A hannu guda masu ganin baiken manufar na ganin tafiyar za ta iya zama wata dabara ta baiwa Amurka damar sarrafa matakan da ya dace kasashen duniya su dauka dangane da batutuwan da suka shafe su baki daya.

Kaza lika, tafiyar za ta zamo tamkar kishiya ga majalisar dinkin duniya, don haka ne ma da yawa daga kasashen Turai suka kaurace mata. In ban da tsirarun kasashe da suka amsa gayyatar da shugaban na Amurka ya mika ta shiga tafiyar da ya kirkiro.

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kwararru da masu nazarin dangantakar kasashen duniya, na ganin burin Trump shi ne mallake ikon fada-a-ji, da tasirin hawan kujerar na ki shi kadai, ta yadda zai rika sarrafa akalar batutuwan kasa da kasa ba tare da raba iko da sauran sassa ba, kuma hakan tamkar komawa salon danniya ne, da mayar da duniya hannun Amurka ita kadai. Matakin da ko alama sassan kasa da kasa ba za su taba lamunta ba! (Saminu Alhassan)

Amurka
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
Daga Birnin Sin

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Next Post
Sin: Ra’ayin Nuna Karfin Soji Zai Jefa Gabas Ta Tsakiya Cikin Mawuyacin Hali

Sin: Ra’ayin Nuna Karfin Soji Zai Jefa Gabas Ta Tsakiya Cikin Mawuyacin Hali

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.