ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Hukuncin Koyon Ilimin Taurari A Shari’a?

by Dakta Jamil Zarewa
6 months ago
Taurari

Assalamu alaikum. Dakta, da fatan an wuni lafiya, Allah ya sa haka, amin.

Akwai wani abu mai kama da ilimi, kuma kamar tsafi ta wata fuskar. A turance, ana kiran sa ‘Astrology’, har akwai makarantun da ake koyar da darasin a Jami’o’i; kama tun daga kan digiri har zuwa digirin digirgir.

Sannan, wasu kuma na amfani da shi a matsayin sana’a; har a ƙasashen waje, ta ɓangarori daban-daban da suka haɗa da bayar da shawarwari.

ADVERTISEMENT
  • Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Taurarin Dan Adam Na Sadarwar Intanet
  • Sin Za Ta Harba Tauraron Dan Adam Samfurin Shenzhou-22

Abin ya dogara ne kacokan a kan sanin taurari, juyawar duniya, rabe-raben ruhi da sauran makamantansu. Sun raba ruhin ɗan’adam gida huɗu, akwai; Ruwa, Ƙasa, Iska da kuma Wuta.

Ko wane ruhi yana tare da wasu taurari waɗanda ake gane su ta hanyar sanin ranar haihuwar mutum. Masu irin waɗannan ilimi, suna iya faɗan halin mutum, wanda kuma a mafi yawancin lokuta yana iya zama daidai.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Suna bayar da shawarwari game da abin da mutum zai yi, har suna faɗa wa mutum cewa, lura da taurari ko makamancin haka, yana da sa’a a wuri kaza ko kuma bashi da sa’a a wuri kaza. Suna kuma faɗar cewa, wane yana da taurarin nasara ko kuma wani abu mai kama da haka.

Ina bibiyar abin a mafi yawancin lokuta, har na fara fahimtar wasu abubuwa game da ilimin. Don haka, mene ne matsayin wannan ilimi a shari’a?

Wa’alaikum assalam. Ɗan’uwa, yin irin wannan nau’i na ilimin taurari haramun ne; yana kuma iya kai wa zuwa ga shirka, saboda Camfi ne da kuma da’awar sanin Gaibu, wanda Allah ya keɓantar da shi.

Imamu Katadah yana cewa, “Allah ya halicci taurari ne, saboda abubuwa guda uku kaɗai:

1- Gane hanya, kamar yadda Allah ya faɗa a suratu Annahl aya ta(16).

2- Ado ga saman duniya.

3- Jifan kangararrun Shaiɗanu masu sato Ji daga sama, Allah maɗaukakin sarki yana cewa a suratul Mulki aya ta (5), “Yin amfani da Taurari wajen gane Nasara ko rashinta, harka ce ta Bokaye, kuma Allah bai tanade su domin yin hakan ba; yana kuma kai wa zuwa ga halaka.

Ya halatta a yi amfani da ilmin Taurari wajen gane Alƙibla da kuma tabbatar da maslahohin addini.

Domin neman ƙarin bayani, duba Alkaulu al-mufid 2/102 da kuma Al-mulakkas fi-sharhi kitabittauhid (236).

Allah ne mafi sani.

Taurari
Dakta Jamil Zarewa
+ postsBio
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Zan Iya Cin Bashin Banki Na Biya Aikin Hajji?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Idan Mace Ta Yi Barin Cikin Wata Biyu, Za Ta Dakatar Da Yin Sallah?
  • Dakta Jamil Zarewa
    https://hausa.leadership.ng/author/dakta-jamil-zarewa/
    Mace Za Ta Iya Yin I’itikafi A Wannan Zamanin?

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
An Bude Cibiyar Yada Labarai Ta Tarukan NPC da CPPCC Ta Bana A Yau Juma’a

An Bude Cibiyar Yada Labarai Ta Tarukan NPC da CPPCC Ta Bana A Yau Juma’a

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.