Mahmud Sadis Buba, wanda aka fi sani da “Al-ajabin Zazzau,” ya janye daga takarar kujerar majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Sabon Gari.
A cikin wata wasiƙa da ya aikewa shugaban jam’iyyar APC na jihar Kaduna, wadda ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Asabar, Buba ya bayyana cewa yanke shawarar janyewar ba abu ne mai sauƙi ba.
Ya ce matakin ya biyo bayan ƙoƙarin sulhu da shugabanni da masu ruwa da tsaki a jam’iyyar suka fara, inda bayan tattaunawa da iyalansa da abokan siyasa ya yanke hukuncin cewa hakan shi ne mafi alheri ga APC.
Buba ya ce haɗa kai a bayan ɗan takara guda shi ne zai ƙarfafa damar nasarar jam’iyyar a babban zaɓe da kuma ci gaban mazabar da jihar baki ɗaya. Ya kuma gode wa gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, da shugabannin jam’iyyar bisa damar da suka ba shi ta shiga takarar.
Ya jaddada cewa janyewarsa ba alamar rauni ba ce, illa sadaukarwa domin muradun jam’iyyar. Haka kuma ya buƙaci magoya bayansa su kwantar da hankalinsu tare da mara wa ɗan takarar da jam’iyyar ta tsayar baya. Tun lokacin da ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takara, Buba ya fuskanci ce-ce-ku-ce kan shekarunsa, inda wasu ke zargin cewa bai kai shekaru 30 ba.















Discussion about this post