ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manema Labarai Kan Manufofi Da Alakar Kasar Da Ketare

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Sin

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gudanar da taron manema labaru yau Lahadi, a gefen taro na hudu na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ta 14, inda ya amsa tambayoyin ‘yan jarida na gida da waje kan manufofin kasar Sin na harkokin waje da huldar kasar da kasashen ketare.

A yayin taron, Wang Yi ya bayyana cewa, “abokantakar da ke tsakanin Sin da Afirka ta yi tsayin daka wajen jure wa jarabtar da ake samu daga sauye-sauyen yanayin kasa da kasa, wanda hakan ya nuna kuzari mai karfi.” Daga ranar 1 ga watan Mayu, kasar Sin za ta fara aiwatar da matakin soke harajin kwastam baki daya a kan kayayyakin da ake biyan haraji a kansu wadanda ake shigo da su daga Afirka.

Kazalika, bisa babban mataki na bude kofar kasar Sin, bangaren Sin zai yi amfani da “cire” harajin wajen bunkasa “karin” cinikayya, da cimma nasarar “rubanya” kyautata rayuwar jama’a, da kuma barin babbar kasuwar kasar Sin ta samar da damammaki ga Afirka.

ADVERTISEMENT

Ban da haka,Wang Yi ya bayyana cewa, a duniyar yau, dimbin kalubalen da suka shafi duniya baki daya na kara bullowa daya-bayan-daya, kuma tsarin bangarori daban-daban na fuskantar kalubale masu tsanani. Shawarar inganta jagorancin duniya (GGI) da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar ta zo a kan lokaci, kuma cikin hanzari ta samu goyon baya da amsa daga kasashe da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 150. Kasar Sin tana kira ga karin kasashe da su shiga a dama da su tare da goyon bayan shawarar ta inganta jagorancin duniya, da yin aiki kafada-da-kafada don farfadowa da kiyayewa, da kuma karfafa MDD.

Duk a wajen taron, Wang Yi ya yi kira da a gaggauta dakatar da bude wuta a yankin Gabas ta Tsakiya domin kare ta’azzarar rikicin da kaucewa yaduwarsa. Ya ce amfani da karfi ba ita ce hanyar warware matsaloli ba, yana mai cewa hakan sabon kiyayya zai haifar. Ya kuma bayyana cewa, kasashe masu tasowa sun zama muhimmin karfin dake ingiza rarrabuwar iko a duniya. Game da dangantakar Sin da Amurka kuma, ya ce ya kamata kasashen biyu su mutunta juna, su kuma rungumi hulda tare cikin lumana.

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Wang Yi ya kara da cewa, shawarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar ta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga bil’adama na da nufin shaida wa duniya cewa makiya bil’adama ba a junansu suke ba, amma su ne yaki, fatara, yunwa, da rashin adalci. Don shawo kan wadannan kalubalen, ba za mu iya dogaro da kokarin daidaikun mutane kadai ba, a’a, wajibi ne mu zama tsintsiya madaurinki daya da kuma yin hadin gwiwa. A zamanin yau, mutane daga dukkan kasashe suna kara fahimtar alfanun zamani da karfin gaskiya da ke tattare da manufar al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga bil’adama.

Wang ya kuma ce, katafariyar bunkasar da kasar Sin ke yi ba za ta taba bin tsohuwar hanya ta nuna karfin iko na babakere da fadada kasa ba, sai dai ma ta bi hanyar samun ci gaba cikin lumana, da sa kaimi ga dukkan kasashen duniya wajen gina duniya mai cike da zaman lafiya mai dorewa, da wadata, da tsafta, da kuma kyau. (Abdulrazaq Yahuza)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Darussa Daga Ramadan Na (1)

Darussa Daga Ramadan Na 15: Kusancin Allah Da Amsar Addu’a A Ramalana

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.