ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manema Labarai Kan Manufofi Da Alakar Kasar Da Ketare

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Sin

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gudanar da taron manema labaru yau Lahadi, a gefen taro na hudu na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ta 14, inda ya amsa tambayoyin ‘yan jarida na gida da waje kan manufofin kasar Sin na harkokin waje da huldar kasar da kasashen ketare.

A yayin taron, Wang Yi ya bayyana cewa, “abokantakar da ke tsakanin Sin da Afirka ta yi tsayin daka wajen jure wa jarabtar da ake samu daga sauye-sauyen yanayin kasa da kasa, wanda hakan ya nuna kuzari mai karfi.” Daga ranar 1 ga watan Mayu, kasar Sin za ta fara aiwatar da matakin soke harajin kwastam baki daya a kan kayayyakin da ake biyan haraji a kansu wadanda ake shigo da su daga Afirka.

Kazalika, bisa babban mataki na bude kofar kasar Sin, bangaren Sin zai yi amfani da “cire” harajin wajen bunkasa “karin” cinikayya, da cimma nasarar “rubanya” kyautata rayuwar jama’a, da kuma barin babbar kasuwar kasar Sin ta samar da damammaki ga Afirka.

ADVERTISEMENT

Ban da haka,Wang Yi ya bayyana cewa, a duniyar yau, dimbin kalubalen da suka shafi duniya baki daya na kara bullowa daya-bayan-daya, kuma tsarin bangarori daban-daban na fuskantar kalubale masu tsanani. Shawarar inganta jagorancin duniya (GGI) da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar ta zo a kan lokaci, kuma cikin hanzari ta samu goyon baya da amsa daga kasashe da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 150. Kasar Sin tana kira ga karin kasashe da su shiga a dama da su tare da goyon bayan shawarar ta inganta jagorancin duniya, da yin aiki kafada-da-kafada don farfadowa da kiyayewa, da kuma karfafa MDD.

Duk a wajen taron, Wang Yi ya yi kira da a gaggauta dakatar da bude wuta a yankin Gabas ta Tsakiya domin kare ta’azzarar rikicin da kaucewa yaduwarsa. Ya ce amfani da karfi ba ita ce hanyar warware matsaloli ba, yana mai cewa hakan sabon kiyayya zai haifar. Ya kuma bayyana cewa, kasashe masu tasowa sun zama muhimmin karfin dake ingiza rarrabuwar iko a duniya. Game da dangantakar Sin da Amurka kuma, ya ce ya kamata kasashen biyu su mutunta juna, su kuma rungumi hulda tare cikin lumana.

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

Wang Yi ya kara da cewa, shawarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar ta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga bil’adama na da nufin shaida wa duniya cewa makiya bil’adama ba a junansu suke ba, amma su ne yaki, fatara, yunwa, da rashin adalci. Don shawo kan wadannan kalubalen, ba za mu iya dogaro da kokarin daidaikun mutane kadai ba, a’a, wajibi ne mu zama tsintsiya madaurinki daya da kuma yin hadin gwiwa. A zamanin yau, mutane daga dukkan kasashe suna kara fahimtar alfanun zamani da karfin gaskiya da ke tattare da manufar al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga bil’adama.

Wang ya kuma ce, katafariyar bunkasar da kasar Sin ke yi ba za ta taba bin tsohuwar hanya ta nuna karfin iko na babakere da fadada kasa ba, sai dai ma ta bi hanyar samun ci gaba cikin lumana, da sa kaimi ga dukkan kasashen duniya wajen gina duniya mai cike da zaman lafiya mai dorewa, da wadata, da tsafta, da kuma kyau. (Abdulrazaq Yahuza)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • Sulaiman
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

MASU ALAKA

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
Daga Birnin Sin

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Next Post
Darussa Daga Ramadan Na (1)

Darussa Daga Ramadan Na 15: Kusancin Allah Da Amsar Addu’a A Ramalana

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.