Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gudanar da taron manema labaru yau Lahadi, a gefen taro na hudu na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ta 14, inda ya amsa tambayoyin ‘yan jarida na gida da waje kan manufofin kasar Sin na harkokin waje da huldar kasar da kasashen ketare.
A yayin taron, Wang Yi ya bayyana cewa, “abokantakar da ke tsakanin Sin da Afirka ta yi tsayin daka wajen jure wa jarabtar da ake samu daga sauye-sauyen yanayin kasa da kasa, wanda hakan ya nuna kuzari mai karfi.” Daga ranar 1 ga watan Mayu, kasar Sin za ta fara aiwatar da matakin soke harajin kwastam baki daya a kan kayayyakin da ake biyan haraji a kansu wadanda ake shigo da su daga Afirka.
Kazalika, bisa babban mataki na bude kofar kasar Sin, bangaren Sin zai yi amfani da “cire” harajin wajen bunkasa “karin” cinikayya, da cimma nasarar “rubanya” kyautata rayuwar jama’a, da kuma barin babbar kasuwar kasar Sin ta samar da damammaki ga Afirka.
Ban da haka,Wang Yi ya bayyana cewa, a duniyar yau, dimbin kalubalen da suka shafi duniya baki daya na kara bullowa daya-bayan-daya, kuma tsarin bangarori daban-daban na fuskantar kalubale masu tsanani. Shawarar inganta jagorancin duniya (GGI) da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar ta zo a kan lokaci, kuma cikin hanzari ta samu goyon baya da amsa daga kasashe da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 150. Kasar Sin tana kira ga karin kasashe da su shiga a dama da su tare da goyon bayan shawarar ta inganta jagorancin duniya, da yin aiki kafada-da-kafada don farfadowa da kiyayewa, da kuma karfafa MDD.
Duk a wajen taron, Wang Yi ya yi kira da a gaggauta dakatar da bude wuta a yankin Gabas ta Tsakiya domin kare ta’azzarar rikicin da kaucewa yaduwarsa. Ya ce amfani da karfi ba ita ce hanyar warware matsaloli ba, yana mai cewa hakan sabon kiyayya zai haifar. Ya kuma bayyana cewa, kasashe masu tasowa sun zama muhimmin karfin dake ingiza rarrabuwar iko a duniya. Game da dangantakar Sin da Amurka kuma, ya ce ya kamata kasashen biyu su mutunta juna, su kuma rungumi hulda tare cikin lumana.
Wang Yi ya kara da cewa, shawarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar ta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga bil’adama na da nufin shaida wa duniya cewa makiya bil’adama ba a junansu suke ba, amma su ne yaki, fatara, yunwa, da rashin adalci. Don shawo kan wadannan kalubalen, ba za mu iya dogaro da kokarin daidaikun mutane kadai ba, a’a, wajibi ne mu zama tsintsiya madaurinki daya da kuma yin hadin gwiwa. A zamanin yau, mutane daga dukkan kasashe suna kara fahimtar alfanun zamani da karfin gaskiya da ke tattare da manufar al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga bil’adama.
Wang ya kuma ce, katafariyar bunkasar da kasar Sin ke yi ba za ta taba bin tsohuwar hanya ta nuna karfin iko na babakere da fadada kasa ba, sai dai ma ta bi hanyar samun ci gaba cikin lumana, da sa kaimi ga dukkan kasashen duniya wajen gina duniya mai cike da zaman lafiya mai dorewa, da wadata, da tsafta, da kuma kyau. (Abdulrazaq Yahuza)















Discussion about this post