ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Manema Labarai Kan Manufofi Da Alakar Kasar Da Ketare

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gudanar da taron manema labaru yau Lahadi, a gefen taro na hudu na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ta 14, inda ya amsa tambayoyin ‘yan jarida na gida da waje kan manufofin kasar Sin na harkokin waje da huldar kasar da kasashen ketare.

A yayin taron, Wang Yi ya bayyana cewa, “abokantakar da ke tsakanin Sin da Afirka ta yi tsayin daka wajen jure wa jarabtar da ake samu daga sauye-sauyen yanayin kasa da kasa, wanda hakan ya nuna kuzari mai karfi.” Daga ranar 1 ga watan Mayu, kasar Sin za ta fara aiwatar da matakin soke harajin kwastam baki daya a kan kayayyakin da ake biyan haraji a kansu wadanda ake shigo da su daga Afirka.

Kazalika, bisa babban mataki na bude kofar kasar Sin, bangaren Sin zai yi amfani da “cire” harajin wajen bunkasa “karin” cinikayya, da cimma nasarar “rubanya” kyautata rayuwar jama’a, da kuma barin babbar kasuwar kasar Sin ta samar da damammaki ga Afirka.

ADVERTISEMENT

Ban da haka,Wang Yi ya bayyana cewa, a duniyar yau, dimbin kalubalen da suka shafi duniya baki daya na kara bullowa daya-bayan-daya, kuma tsarin bangarori daban-daban na fuskantar kalubale masu tsanani. Shawarar inganta jagorancin duniya (GGI) da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar ta zo a kan lokaci, kuma cikin hanzari ta samu goyon baya da amsa daga kasashe da kungiyoyin kasa da kasa fiye da 150. Kasar Sin tana kira ga karin kasashe da su shiga a dama da su tare da goyon bayan shawarar ta inganta jagorancin duniya, da yin aiki kafada-da-kafada don farfadowa da kiyayewa, da kuma karfafa MDD.

Duk a wajen taron, Wang Yi ya yi kira da a gaggauta dakatar da bude wuta a yankin Gabas ta Tsakiya domin kare ta’azzarar rikicin da kaucewa yaduwarsa. Ya ce amfani da karfi ba ita ce hanyar warware matsaloli ba, yana mai cewa hakan sabon kiyayya zai haifar. Ya kuma bayyana cewa, kasashe masu tasowa sun zama muhimmin karfin dake ingiza rarrabuwar iko a duniya. Game da dangantakar Sin da Amurka kuma, ya ce ya kamata kasashen biyu su mutunta juna, su kuma rungumi hulda tare cikin lumana.

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Wang Yi ya kara da cewa, shawarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar ta gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga bil’adama na da nufin shaida wa duniya cewa makiya bil’adama ba a junansu suke ba, amma su ne yaki, fatara, yunwa, da rashin adalci. Don shawo kan wadannan kalubalen, ba za mu iya dogaro da kokarin daidaikun mutane kadai ba, a’a, wajibi ne mu zama tsintsiya madaurinki daya da kuma yin hadin gwiwa. A zamanin yau, mutane daga dukkan kasashe suna kara fahimtar alfanun zamani da karfin gaskiya da ke tattare da manufar al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga bil’adama.

Wang ya kuma ce, katafariyar bunkasar da kasar Sin ke yi ba za ta taba bin tsohuwar hanya ta nuna karfin iko na babakere da fadada kasa ba, sai dai ma ta bi hanyar samun ci gaba cikin lumana, da sa kaimi ga dukkan kasashen duniya wajen gina duniya mai cike da zaman lafiya mai dorewa, da wadata, da tsafta, da kuma kyau. (Abdulrazaq Yahuza)

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Sulaiman
    Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Sulaiman
    Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
  • Sulaiman
    Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

MASU ALAKA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Next Post
Darussa Daga Ramadan Na (1)

Darussa Daga Ramadan Na 15: Kusancin Allah Da Amsar Addu’a A Ramalana

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Sin

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Sin

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Sin

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.