ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 15: Kusancin Allah Da Amsar Addu’a A Ramalana

by Nuhu Ubale Ibrahim
4 months ago
Ramadan

A watan Ramalana muna ƙara fahimtar cewa Allah Maɗaukaki Yana kusa da mu da iliminsa, kusa da jinsa, kusa da taimakonsa da rahamarsa. Ba kusanci na tazara ba ne, amma kusanci ne na kulawa da amsa addu’a da kiran da ake yi masa tsarki ya tabbata a gare Shi.

A tsakiyar ayoyin azumi, Allah Ya kawo wata aya mai cike da ta’aziyya da bege. Ya ce a cikin Alƙur’ani, a Suratul Baƙara aya ta ( 186): “Kuma idan bayina suka tambaye ka dangane da Ni, to, lalle Ni kusa Nake. Ina amsa kiran mai kira idan ya kiraye Ni. Don haka su amsa Mini kiran, kuma su yi imani da Ni, domin su shiryu”

  • Darussa Daga Ramadan Na 14: Yawaita Kyauta Da Ihsani A Ramalana
  • Darussa Daga Ramadan Na 13: Tsayuwar Dare

Ka lura da yadda ayar ta zo kai tsaye; ba a ce “Ka ce musu Ina kusa” ba; Allah Ya ce “Ni kusa Nake”. Wannan yana nuna kusanci na musamman, kusancin rahama, da kusancin jin ƙorafi, kusancin amsa koke.

ADVERTISEMENT

Ramalana wata ne da wannan kusanci yake bayyana sosai. Zuciya tana laushi, hawaye suna sauƙin zuba, addu’a tana fitowa daga zurfin ran bil’adama. Mumini yana jin cewa babu shamaki tsakaninsa da Ubangijinsa.

Wannan aya ta ƙunshi manyan darussa:

LABARAI MASU NASABA

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

1. Allah Yana kusa da bayi: babu buƙatar mai shiga tsakani wajen roƙonsa.
2. Yana amsa addu’a: komai girman buƙata ko ƙarancinta.
3. Akwai sharaɗi na amsa addu’a: shi ne “su amsa Mini kiran” watau su yi biyayya ga umarninsa.
3. Imani shi ne hanyar shiriya: duk wanda ya yi imani da gaske, zai samu jagoranci.

Saboda haka, karɓuwar addu’a tana da alaƙa da biyayya. Idan bawa yana so Allah Ya amsa masa, shi ma ya amsa wa Allah ta hanyar aikata umarni da nisantar hani.

Ramalana yana koya mana cewa Allah ba Ya nesa. Idan damuwa ta yi yawa, Yana kusa. Idan buƙata ta yi girma, Yana kusa. Idan zuciya ta karye, Yana kusa. Kuma Yana jin kukan bawa ko da a cikin dare ne mai zurfi Fahimtr haka; tana haifar da kwanciyar hankali. Domin wanda ya san Allah Yana kusa, ba ya yanke ƙauna. Wanda ya san Allah Yana ji, ba ya jin shi kaɗai ne. Wanda ya san Allah Yana amsawa, ba ya daina addu’a.

Saboda haka, mu yawaita kiran Sa a Ramalana. Mu roƙe Shi da zuciya mai ƙasƙantar da kai. Mu haɗa addu’a da biyayya. Mu haɗa bege da tsoron Allah.

Allah Ya sa mu kasance cikin masu gane kusancinsa, masu amsa kiransa, masu samun amsar addu’a da shiriya a duniya da Lahira. Amin.

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
Ilimi

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
Ilimi

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Next Post
Gwamnatin Kebbi Ta Yi Rabon Kayan Aikin Noman Rani

Gwamnatin Kebbi Ta Yi Rabon Kayan Aikin Noman Rani

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.