ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 15: Kusancin Allah Da Amsar Addu’a A Ramalana

by Nuhu Ubale Ibrahim
3 months ago
Ramadan

A watan Ramalana muna ƙara fahimtar cewa Allah Maɗaukaki Yana kusa da mu da iliminsa, kusa da jinsa, kusa da taimakonsa da rahamarsa. Ba kusanci na tazara ba ne, amma kusanci ne na kulawa da amsa addu’a da kiran da ake yi masa tsarki ya tabbata a gare Shi.

A tsakiyar ayoyin azumi, Allah Ya kawo wata aya mai cike da ta’aziyya da bege. Ya ce a cikin Alƙur’ani, a Suratul Baƙara aya ta ( 186): “Kuma idan bayina suka tambaye ka dangane da Ni, to, lalle Ni kusa Nake. Ina amsa kiran mai kira idan ya kiraye Ni. Don haka su amsa Mini kiran, kuma su yi imani da Ni, domin su shiryu”

  • Darussa Daga Ramadan Na 14: Yawaita Kyauta Da Ihsani A Ramalana
  • Darussa Daga Ramadan Na 13: Tsayuwar Dare

Ka lura da yadda ayar ta zo kai tsaye; ba a ce “Ka ce musu Ina kusa” ba; Allah Ya ce “Ni kusa Nake”. Wannan yana nuna kusanci na musamman, kusancin rahama, da kusancin jin ƙorafi, kusancin amsa koke.

ADVERTISEMENT

Ramalana wata ne da wannan kusanci yake bayyana sosai. Zuciya tana laushi, hawaye suna sauƙin zuba, addu’a tana fitowa daga zurfin ran bil’adama. Mumini yana jin cewa babu shamaki tsakaninsa da Ubangijinsa.

Wannan aya ta ƙunshi manyan darussa:

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

1. Allah Yana kusa da bayi: babu buƙatar mai shiga tsakani wajen roƙonsa.
2. Yana amsa addu’a: komai girman buƙata ko ƙarancinta.
3. Akwai sharaɗi na amsa addu’a: shi ne “su amsa Mini kiran” watau su yi biyayya ga umarninsa.
3. Imani shi ne hanyar shiriya: duk wanda ya yi imani da gaske, zai samu jagoranci.

Saboda haka, karɓuwar addu’a tana da alaƙa da biyayya. Idan bawa yana so Allah Ya amsa masa, shi ma ya amsa wa Allah ta hanyar aikata umarni da nisantar hani.

Ramalana yana koya mana cewa Allah ba Ya nesa. Idan damuwa ta yi yawa, Yana kusa. Idan buƙata ta yi girma, Yana kusa. Idan zuciya ta karye, Yana kusa. Kuma Yana jin kukan bawa ko da a cikin dare ne mai zurfi Fahimtr haka; tana haifar da kwanciyar hankali. Domin wanda ya san Allah Yana kusa, ba ya yanke ƙauna. Wanda ya san Allah Yana ji, ba ya jin shi kaɗai ne. Wanda ya san Allah Yana amsawa, ba ya daina addu’a.

Saboda haka, mu yawaita kiran Sa a Ramalana. Mu roƙe Shi da zuciya mai ƙasƙantar da kai. Mu haɗa addu’a da biyayya. Mu haɗa bege da tsoron Allah.

Allah Ya sa mu kasance cikin masu gane kusancinsa, masu amsa kiransa, masu samun amsar addu’a da shiriya a duniya da Lahira. Amin.

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Gwamnatin Kebbi Ta Yi Rabon Kayan Aikin Noman Rani

Gwamnatin Kebbi Ta Yi Rabon Kayan Aikin Noman Rani

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.