ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussa Daga Ramadan Na 15: Kusancin Allah Da Amsar Addu’a A Ramalana

by Nuhu Ubale Ibrahim
5 months ago
Ramadan

A watan Ramalana muna ƙara fahimtar cewa Allah Maɗaukaki Yana kusa da mu da iliminsa, kusa da jinsa, kusa da taimakonsa da rahamarsa. Ba kusanci na tazara ba ne, amma kusanci ne na kulawa da amsa addu’a da kiran da ake yi masa tsarki ya tabbata a gare Shi.

A tsakiyar ayoyin azumi, Allah Ya kawo wata aya mai cike da ta’aziyya da bege. Ya ce a cikin Alƙur’ani, a Suratul Baƙara aya ta ( 186): “Kuma idan bayina suka tambaye ka dangane da Ni, to, lalle Ni kusa Nake. Ina amsa kiran mai kira idan ya kiraye Ni. Don haka su amsa Mini kiran, kuma su yi imani da Ni, domin su shiryu”

  • Darussa Daga Ramadan Na 14: Yawaita Kyauta Da Ihsani A Ramalana
  • Darussa Daga Ramadan Na 13: Tsayuwar Dare

Ka lura da yadda ayar ta zo kai tsaye; ba a ce “Ka ce musu Ina kusa” ba; Allah Ya ce “Ni kusa Nake”. Wannan yana nuna kusanci na musamman, kusancin rahama, da kusancin jin ƙorafi, kusancin amsa koke.

ADVERTISEMENT

Ramalana wata ne da wannan kusanci yake bayyana sosai. Zuciya tana laushi, hawaye suna sauƙin zuba, addu’a tana fitowa daga zurfin ran bil’adama. Mumini yana jin cewa babu shamaki tsakaninsa da Ubangijinsa.

Wannan aya ta ƙunshi manyan darussa:

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

1. Allah Yana kusa da bayi: babu buƙatar mai shiga tsakani wajen roƙonsa.
2. Yana amsa addu’a: komai girman buƙata ko ƙarancinta.
3. Akwai sharaɗi na amsa addu’a: shi ne “su amsa Mini kiran” watau su yi biyayya ga umarninsa.
3. Imani shi ne hanyar shiriya: duk wanda ya yi imani da gaske, zai samu jagoranci.

Saboda haka, karɓuwar addu’a tana da alaƙa da biyayya. Idan bawa yana so Allah Ya amsa masa, shi ma ya amsa wa Allah ta hanyar aikata umarni da nisantar hani.

Ramalana yana koya mana cewa Allah ba Ya nesa. Idan damuwa ta yi yawa, Yana kusa. Idan buƙata ta yi girma, Yana kusa. Idan zuciya ta karye, Yana kusa. Kuma Yana jin kukan bawa ko da a cikin dare ne mai zurfi Fahimtr haka; tana haifar da kwanciyar hankali. Domin wanda ya san Allah Yana kusa, ba ya yanke ƙauna. Wanda ya san Allah Yana ji, ba ya jin shi kaɗai ne. Wanda ya san Allah Yana amsawa, ba ya daina addu’a.

Saboda haka, mu yawaita kiran Sa a Ramalana. Mu roƙe Shi da zuciya mai ƙasƙantar da kai. Mu haɗa addu’a da biyayya. Mu haɗa bege da tsoron Allah.

Allah Ya sa mu kasance cikin masu gane kusancinsa, masu amsa kiransa, masu samun amsar addu’a da shiriya a duniya da Lahira. Amin.

Ramadan
Nuhu Ubale Ibrahim
+ postsBio
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    Karamar Sallah: Sallar Idi A Wajen Musulmi…
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 23
  • Nuhu Ubale Ibrahim
    https://hausa.leadership.ng/author/nuhu-ubale-ibrahim/
    SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 22

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Ilimi

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
Ilimi

ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus

July 3, 2026
Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa
Fatawa

Menene Hukuncin Yin Aure Da Cikin Shege?

June 21, 2026
Next Post
Gwamnatin Kebbi Ta Yi Rabon Kayan Aikin Noman Rani

Gwamnatin Kebbi Ta Yi Rabon Kayan Aikin Noman Rani

LABARAI MASU NASABA

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

Yadda Kotun Daukaka Kara Ta Kama Hanyar Cin Gashin Kanta

July 24, 2026
Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

Yadda ‘Yan Spain Suka Mamaye Kyaututtukan Kofin Duniya

July 24, 2026
Ramadan

Wasiƙar Trump Ba Za Ta Ceto Tinubu Daga Faduwa Zaɓe Ba – Jam’iyyar ADC

July 24, 2026
Falalar Yawaita Istigifari (2)

Falalar Yawaita Istigifari (2)

July 24, 2026
Ramadan

Amurka Ta Kakaba Harajin Kaso 12.5% A Kan kayayyakin Nijeriya

July 24, 2026
Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

Wane Ne Gwarzo Tsakanin Pele Da Maradona Da Messi?

July 24, 2026
Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

July 24, 2026
NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

July 24, 2026
Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.