Memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi, ya zanta da takwaransa na kasar Iran Seyed Abbas Araghchi ta waya, jiya Laraba 17 ga watan nan.A zantawarsu, Araghchi ya bayyana yadda Iran da Amurka suka cimma yarjejeniyar samun fahimtar juna ta matakin farko, da gode wa kasar Sin saboda rawar a-zo-a-gani da ta taka wurin taimakawa gudanar da shawarwari tare kuma da cimma yarjejeniya.
A cewarsa, ya dace a aiwatar da yarjejeniyar a zahiri, ciki har da dakatar da matakan soji da Isra’ila ke dauka kan Lebanon. Ya ce kasar Iran tana tsayawa ga raya dangantaka tare da kasar Sin bisa manyan tsare-tsare, inda ta yi fatan kara samun fahimtar juna tsakanin kasashen biyu, da zurfafa hadin gwiwa a bangarori daban-daban, a wani kokari na ingiza ci gaban dangantakar abotarsu daga dukkan fannoni kuma bisa manyan tsare-tsare.Sai kuma a nasa bangaren, Wang Yi ya ce, kasarsa ta yi maraba da yarjejeniyar samun fahimtar juna ta matakin farko da aka cimma tsakanin Iran da Amurka, inda a cewarsa, lokacin cimma zaman lafiya ya yi, kuma abu mai muhimmanci a nan gaba shi ne bangarori masu ruwa da tsaki su dauki matakai na zahiri don cika alkawarinsu, da kawar da cikas daga fannoni daban-daban.
Ya ce kasar Sin tana goyon-bayan Iran wajen kyautata dangantaka da kasashen shiyyar, da neman dabarun kafa tsarin zaman lafiya na shiyyarsu. Wang ya kara da cewa, kasarsa tana fatan inganta mu’amala da tuntuba da Iran, don ci gaba da bayar da gudummawa ga kiyayewa gami da kara samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a shiyyar, yayin da kasashen biyu ke bunkasa dangantakarsu. (Murtala Zhang)















Discussion about this post