ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Iran Sun Zanta Ta Waya

by Sulaiman
52 minutes ago
Sin

LABARAI MASU NASABA

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

Memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi, ya zanta da takwaransa na kasar Iran Seyed Abbas Araghchi ta waya, jiya Laraba 17 ga watan nan.A zantawarsu, Araghchi ya bayyana yadda Iran da Amurka suka cimma yarjejeniyar samun fahimtar juna ta matakin farko, da gode wa kasar Sin saboda rawar a-zo-a-gani da ta taka wurin taimakawa gudanar da shawarwari tare kuma da cimma yarjejeniya.

A cewarsa, ya dace a aiwatar da yarjejeniyar a zahiri, ciki har da dakatar da matakan soji da Isra’ila ke dauka kan Lebanon. Ya ce kasar Iran tana tsayawa ga raya dangantaka tare da kasar Sin bisa manyan tsare-tsare, inda ta yi fatan kara samun fahimtar juna tsakanin kasashen biyu, da zurfafa hadin gwiwa a bangarori daban-daban, a wani kokari na ingiza ci gaban dangantakar abotarsu daga dukkan fannoni kuma bisa manyan tsare-tsare.Sai kuma a nasa bangaren, Wang Yi ya ce, kasarsa ta yi maraba da yarjejeniyar samun fahimtar juna ta matakin farko da aka cimma tsakanin Iran da Amurka, inda a cewarsa, lokacin cimma zaman lafiya ya yi, kuma abu mai muhimmanci a nan gaba shi ne bangarori masu ruwa da tsaki su dauki matakai na zahiri don cika alkawarinsu, da kawar da cikas daga fannoni daban-daban.

Ya ce kasar Sin tana goyon-bayan Iran wajen kyautata dangantaka da kasashen shiyyar, da neman dabarun kafa tsarin zaman lafiya na shiyyarsu. Wang ya kara da cewa, kasarsa tana fatan inganta mu’amala da tuntuba da Iran, don ci gaba da bayar da gudummawa ga kiyayewa gami da kara samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a shiyyar, yayin da kasashen biyu ke bunkasa dangantakarsu. (Murtala Zhang)

ADVERTISEMENT
Sin
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sarkin Kano Sanusi II Ya Ce Tsauraran Sharuɗɗan Beli Ne Ke Jinkirta Sakin El-Rufai
  • Sulaiman
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Sulaiman
    Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar
  • Sulaiman
    Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

MASU ALAKA

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar
Daga Birnin Sin

Xi: Sin Na Gudanar Da Ayyukan Hadin Gwiwa Tsakanin Yankunan Gabashi Da Yammacin Kasar

June 17, 2026
Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Tallafin Jin Kai Na Gaggawa Ga DRC Da AU

June 17, 2026
Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku
Daga Birnin Sin

Fahimtar Tattalin Arzikin Sin Na Watannin Biyar Na Farkon Bana Ta Kalmomi Guda Uku

June 17, 2026
Next Post
CBN

Sarkin Kano Sanusi II Ya Ce Tsauraran Sharuɗɗan Beli Ne Ke Jinkirta Sakin El-Rufai

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

CBN

Sarkin Kano Sanusi II Ya Ce Tsauraran Sharuɗɗan Beli Ne Ke Jinkirta Sakin El-Rufai

June 18, 2026
Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Iran Sun Zanta Ta Waya

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Iran Sun Zanta Ta Waya

June 18, 2026
Shigo Da Fetur Ya Ƙaru Da Kashi 59.5% A Watan Mayu A Nijeriya — NMDPRA

Shigo Da Fetur Ya Ƙaru Da Kashi 59.5% A Watan Mayu A Nijeriya — NMDPRA

June 18, 2026
Gwamnatin Kwara Ta Kai Saraki Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamna AbdulRazaq

Gwamnatin Kwara Ta Kai Saraki Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamna AbdulRazaq

June 18, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

2027: Tsohon Kakakin Majalisar Kaduna Abdulfatah Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan PRP

June 18, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

Sojoji Sun Ceto Mutane 5 Da Aka Sace A Kogi

June 18, 2026
Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

Kotu A Birtaniya Ta Wanke Diezani Daga Zargin Cin Hanci

June 18, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya, Sun Sace Limami Da Wasu Mutane 7 A Filato

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gwande A Jihar Filato

June 18, 2026
Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

Matsalar Tsaro: Davido Ya Mayar Wa Rarara Martani Kan Rashin Tsaro

June 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.