Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya bayyana cewa tsauraran sharuɗɗan beli da aka gindaya wa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai, ne ke jinkirta sakin sa daga hannun Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifuka Masu Alaƙa da Hakan (ICPC).
Sanusi ya yi wannan ikirari ne yayin da yake zantawa da manema labarai bayan wani taro, inda ya bayyana cewa sharuɗɗan da aka sanya domin a saki El-Rufai suna da matuƙar wahalar cikawa.
A cewarsa, waɗannan sharuɗɗa sun sa ƙoƙarin tabbatar da sakin tsohon gwamnan ya gamu da ƙalubale.Sanusi ya ce, “Misali, ku dubi abin da ke faruwa da ɗan’uwana, Malam Nasir El-Rufai. A halin yanzu yana tsare, kuma sharuɗɗan da aka gindaya domin a sake shi suna da matuƙar wahala.
“An ce dole sai wani sarki da kuma wani babban jami’in gwamnati sun sanya hannu a takardun belinsa kafin a sake shi.”
Sarkin ya nuna damuwarsa kan irin waɗannan sharuɗɗa, yana mai cewa suna ƙara wahalar da tsarin samun beli ga El-Rufai














Discussion about this post