ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mota Ta Kaɗe Masu Tattakin Kirsimeti 22 A Gombe

by Sadiq
2 years ago
Kirsimeti

Wani hatsarin mota ya jikkata mutane 22 da ke tattakin bikin Kirsimeti a Gombe, babban birnin Jihar Gombe.

Lamarin ya faru ne da safiyar Laraba, lokacin da mabiya addinin Kirista ke gudanar da tattaki a cikin garin, kamar yadda suka saba duk shekara.

  • Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Goge Munanan Abubuwan Da Suka Shafi Kasar Sin A Cikin Kudurin Manufofin Tsaro Na Shekara-shekara
  • Kirismeti: NDLEA Ta Cafke Mutane 34 A Wuraren Sayar Da Miyagun Kwayoyi A Kano 

Kakakin ’yansandan Jihar Gombe, ASP Buhari Abdullahi, ya ce wata mota ƙirar Sharon da aka loda wa kayan hatsi ta afka cikin masu tattakin daga baya, ta buge mutane da dama.

ADVERTISEMENT

“Mutane da dama sun ji raunuka, wasu ma har da karaya, kuma an garzaya da su zuwa asibiti don samun kulawa,” in ji ASP Abdullahi.

Ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun ceci direban motar daga hannun mutane da suka yi yunkurin dukansa, wanda hakan ya kusa haddasa tashin hankali.

LABARAI MASU NASABA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Duk da wannan hatsari, masu tattakin sun kammala shirin da suka tsara na bikin Kirsimeti cikin nasara.

A ranar Laraba, mabiya addinin Kirista a faɗin duniya suka yi murnar zagayowar ranar haihuwar Yesu Almasihu.

Bikin Kirsimeti ya gudana cikin lumana a yawancin wurare a Nijeriya, ba tare da rahoton wani tashin hankali ba.

Sai dai gabanin bikin, an samu rahoton turmutsitsin rabon abinci a Abuja da jihohin Anambra da Oyo, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da yawa.

A Okija, Jihar Anambra, mutum 22 sun rasa rayukansu; a Abuja, mutum 10 ne suka mutu, yayin da a garin Ibadan, Jihar Oyo, yara 35 suka mutu a turmutsitsin.

MASU ALAKA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe
Labarai

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa
Labarai

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

June 27, 2026
Next Post
‘Yansandan Ƙasa Da Ƙasa Na Neman ‘Yan Nijeriya 14 Saboda Laifuka

'Yansandan Ƙasa Da Ƙasa Na Neman 'Yan Nijeriya 14 Saboda Laifuka

LABARAI MASU NASABA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

June 27, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

June 27, 2026
Kirsimeti

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 27, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.