ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mota Ta Kaɗe Masu Tattakin Kirsimeti 22 A Gombe

by Sadiq
2 years ago
Kirsimeti

Wani hatsarin mota ya jikkata mutane 22 da ke tattakin bikin Kirsimeti a Gombe, babban birnin Jihar Gombe.

Lamarin ya faru ne da safiyar Laraba, lokacin da mabiya addinin Kirista ke gudanar da tattaki a cikin garin, kamar yadda suka saba duk shekara.

  • Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Goge Munanan Abubuwan Da Suka Shafi Kasar Sin A Cikin Kudurin Manufofin Tsaro Na Shekara-shekara
  • Kirismeti: NDLEA Ta Cafke Mutane 34 A Wuraren Sayar Da Miyagun Kwayoyi A Kano 

Kakakin ’yansandan Jihar Gombe, ASP Buhari Abdullahi, ya ce wata mota ƙirar Sharon da aka loda wa kayan hatsi ta afka cikin masu tattakin daga baya, ta buge mutane da dama.

ADVERTISEMENT

“Mutane da dama sun ji raunuka, wasu ma har da karaya, kuma an garzaya da su zuwa asibiti don samun kulawa,” in ji ASP Abdullahi.

Ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun ceci direban motar daga hannun mutane da suka yi yunkurin dukansa, wanda hakan ya kusa haddasa tashin hankali.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Duk da wannan hatsari, masu tattakin sun kammala shirin da suka tsara na bikin Kirsimeti cikin nasara.

A ranar Laraba, mabiya addinin Kirista a faɗin duniya suka yi murnar zagayowar ranar haihuwar Yesu Almasihu.

Bikin Kirsimeti ya gudana cikin lumana a yawancin wurare a Nijeriya, ba tare da rahoton wani tashin hankali ba.

Sai dai gabanin bikin, an samu rahoton turmutsitsin rabon abinci a Abuja da jihohin Anambra da Oyo, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da yawa.

A Okija, Jihar Anambra, mutum 22 sun rasa rayukansu; a Abuja, mutum 10 ne suka mutu, yayin da a garin Ibadan, Jihar Oyo, yara 35 suka mutu a turmutsitsin.

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
‘Yansandan Ƙasa Da Ƙasa Na Neman ‘Yan Nijeriya 14 Saboda Laifuka

'Yansandan Ƙasa Da Ƙasa Na Neman 'Yan Nijeriya 14 Saboda Laifuka

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.