ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane Kimanin Miliyan 135 Sun Yi Yawon Shakatawa A Yayin Hutun Bikin Sabuwar Shekara A Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
Yawon shakatawa

Jiya Litinin, ma’aikatar harkokin aladu da yawon shakatawa ta kasar Sin, ta fidda bayani game da kasuwannin raya aladu da yawon shakatawa, a lokacin hutun bikin sabuwar shekarar nan ta 2024. 

Kididdigar da cibiyar bayanai ta maaikatar ta fitar ta nuna cewa, a yayin hutun kwanaki 3 na bikin sabuwar shekara, mutane kimanin miliyan 135 sun yi tafiye-tafiye na yawon shakatawa a kasar Sin, adadin da ya karu da kaso 155.3 bisa dari idan aka kwatanta da na makamancin lokaci na bara, kuma adadin ya karu da kaso 9.4 bisa dari idan aka kwatanta da na makamancin lokaci na shekarar 2019.

  • Adadin Wayoyin Salula Da Kamfanonin Kirar Su Suka Fitar A Kasar Sin Ya Karu Da 34.3% A Watan Nuwamba
  • Xi Jinping Ya Gana Da Jakadun Kasar Sin Dake Kasashen Waje Wadanda Suka Dawo Beijing Don Halartar Taro

Kaza lika hakan ya sa an samu kudin shiga kimanin Yuan biliyan 79 da miliyan 730, a harkokin yawon shakatawa a kasar ta Sin, adadin da ya karu da kaso 200.7 bisa dari idan aka kwatanta da na makamancin lokaci na bara, wanda ya kuma karu da kaso 5.6 bisa dari idan aka kwatanta da na makamancin lokaci na shekarar 2019.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, a yayin hutun bikin sabuwar shekarar, an gudanar da ayyuka masu nasaba da aladu da yawon shakatawa yadda ya kamata a duk fadin kasar Sin.

A lokacin hutun, mazauna birane da kauyuka sun nuna kuzarin tafi yawon shakatawa, musamman ma zuwa wuraren wasa da kankara da na dusar kankara, a maimakon tafiya wuraren yawon shakatawa na gargajiya. A halin yanzu, mutane sun fi son tafiya wuraren shan iska cikin birane da wuraren wasanni na musamman.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Tsoffi da masu matsakaitan shekaru, da mazauna kauyuka, da kuma mutanen dake zama cikin kanana da matsakaicin birane, sun nuna kuzarin tafiya yawon shakatawa. Cikin wadanda suka yi yawon shakatawa, an samu karuwar adadin tsoffi, da masu matsakaitan shekaru, da mutanen dake zaune a kauyuka, da kuma mazauna kanana da matsakaitan birane, lamarin da ya yi muhimmin tasiri ga kasuwannin yawon shakatawa.

Bayanin da cibiyar bayanai ta maaikatar harkokin aladu da yawon shakatawa ta kasar Sin ta fidda, ya nuna cewa, cikin farkon kwanaki biyu na hutun bikin sabuwar shekarar, yawan mutanen da suka tafi yawon shakatawa daga yankunan karkara ya kai kaso 4.2 bisa dari, adadin da ya kai kaso 20 bisa dari bisa yawan alummar da suka yi yawon shakatawa a cikin kasar Sin, kuma adadin da ya kai matsayin da ba a taba gani ba a yayin hutun bikin sabuwar shekara. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

Yawon shakatawa
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
nahcon

Da Dumi-dumi: NAHCON Ta Kara Wa'adin Biyan Kujerar Aikin Hajjin 2024

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.