Aƙalla mutum shida ne suka rasu yayin da wasu shida suka jikkata sakamakon fashewar wani bam da aka dasa a gefen hanya a kan titin Bagega zuwa Anka a Jihar Zamfara.
Lamarin ya faru ne da safiyar ranar Alhamis lokacin da wata mota ɗauke da fasinjoji ke wucewa ta yankin da ke ƙaramar hukumar Anka.
Majiyoyi daga yankin sun ce ana zargin ’yan bindiga ne suka dasa bam ɗin.
Fashewar ta lalata motar tare da tayar da hankalin mazauna yankin da masu amfani da hanyar.
Wani mazaunin garin Bagega ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 9 na safe, inda ya bayyana cewa wasu daga cikin fasinjojin sun mutu nan take yayin da wasu suka samu munanan raunuka.
Kakakin rundunar ’yansandan jihar, DSP Yazid Abubakar, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa mutum shida sun mutu yayin da wasu shida ke karɓar magani a asibiti.
Ya ƙara da cewa an tura jami’an tsaro zuwa yankin kuma al’amura sun koma daidai.















Discussion about this post