Kasar Uganda ta bayyana bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da fitar da su daga kasar Sin na kasa da kasa na Canton Fair, a matsayin muhimmin dandalin bunkasa hadin gwiwar ciniki da zuba jari.
Cikin wata sanarwa, gwamnatin Uganda ta ce halartar baje kolin a birnin Guangzhou na lardin Guangdong, na da nufin fadada fitar da kayayyakin kasar, da jan hankalin jarin waje da zurfafa dangantakar tattalin arziki musammam da kasar Sin.
Masu baje koli na Uganda da dama ne suka baje hajojinsu da suka hada da kofi da man kadanya da kayayyakin hannu, yayin kashi na 3 na baje kolin wanda ya gudana daga ranar 1 zuwa 5 ga watan nan na Mayu. Haka kuma, bangaren yawon bude ido na kasar ya ja hankalin baki mahalartar baje kokin.
Halartar Uganda baje kolin ya zo ne a daidai lokacin da ake samun karuwar cinikayya tsakaninta da Sin. Alkaluma daga ma’aikatar kula da harkokin wajen Sin sun nuna cewa, darajar cinikayya tsakanin kasashen biyu ta kai dalar Amurka biliyan 2.1 a shekarar 2025, wadda ta karu da kaso 43.5 a mizanin shekara-shekara, kana ta kafa sabon tarihi. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post