Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, ya ce a bayyane take babu wani mukami a yanzu na shugaban kasar Taiwan a duniya. Kuma duk masu nada kansu wannan mukami na karya, suna karyata tarihi tare da jawo wa kansu kaskanci.
Kakakin ya bayyana hakan ne a Larabar nan, bayan da mahukuntan yankin Taiwan suka dage ziyarar da aka tsara Lai Ching-te zai gudanar a Eswatini.
A cewar jami’in, dukkanin kasashen nahiyar Afirka 53 in ban da Eswatini sun kulla huldar diflomasiyya da kasar Sin.
Sun kuma sha nanata amincewa da kasar Sin daya tak a duniya, da kuma matsayin Taiwan na bangaren Sin da ba za a iya balle shi ba, kana sun yarda da jamhuriyar jama’ar kasar Sin a matsayin gwamnati daya tilo dake wakiltar daukacin yankunan kasar.
Kazalika, amincewar kasashen da lamarin ya shafa da ka’idar kasar Sin daya tak a duniya, ya yi daidai da dokokin kasa da kasa, da ka’idojin cudanyar kasashen duniya. Matakin da kasar Sin ke matukar yabawa da shi. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post