Rundunar sojin sama ta haɗin gwiwa ta ‘Operation Hadin Kai’ ta kashe ’yan ta’adda 27 a wasu hare-haren sama da aka kai kan maɓoyar ’yan ta’adda a yankunan Kudanci da Arewacin Tumbus na jihar Borno.
Rahoton da rundunar sojin saman Nijeriya (NAF) ta fitar wanda kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) ya sanar a ranar Lahadi ya nuna cewa, an gudanar da hare-haren ne bayan tattara bayanan sirri da sa ido ta sama (ISR) a yankunan da aka kai hare-haren.
A cewar rahoton, jiragen yaƙi na Dragon da jiragen tattara bayanan sirri sun kai hari a Dawoshe, wata sananniyar maɓoyar ’yan ta’adda da ke yankin Kudancin Tumbus, da misalin ƙarfe 12:40 na dare a ranar 10 ga Yuni.
Rahoton ya bayyana cewa an hango motocin ’yan ta’addan yayin sintirin sama, sannan jiragen yaƙin suka kai musu hari.
Ya ƙara da cewa binciken bayanan bayan harin, ya tabbatar da cewa an lalata motocin gaba ɗaya, yayin da aka kashe ’yan ta’adda 12 a wannan samamen.
Rundunar ta ce sauran hare-haren da aka kai a wasu maɓoyar ’yan ta’addan a yankin Tumbus sun kai ga kashe jimillar ’yan ta’adda 27, a wani mataki na ci gaba da matsa lamba kan ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya a yankin Arewa maso Gabas.














Discussion about this post