Hukumar Alhazai ta Ƙasa, (NAHCON), ta karyata ikirarin da ke yadawa cewa, Nijeriya ta ƙi karɓar ƙarin kujerun Hajji 20,000, tana mai bayyana labarin a matsayin mara tushe.
Hukumar ta bayyana cewa raguwar adadin maniyyatan Hajji daga kusan 95,000 zuwa 50,000 ba sakamakon wani zaɓi bane na NAHCON, illa dai yana da alaƙa kai tsaye da sabbin manufofi da hukumar Kula da Aikin Hajji da Umrah ta kasar Saudi ta aiwatar.
A watan Disamba 2025, hukumomin Saudiyya sun ƙaddamar da wani tsarin rage yawan guraben Hajji a faɗin duniya. Wannan mataki ya zo ne domin rage cunkoso da kuma inganta tsaron lafiyar alhazai daga ƙasashe daban-daban.
Nijeriya, kamar sauran ƙasashe, ta fuskanci tasirin wannan sabon tsari.Sabanin ra’ayoyin da ke yawo cewa an ƙi karɓar ƙarin guraben, NAHCON ta bayyana cewa ta gabatar da buƙatu da dama ga hukumomin Saudiyya domin ƙara wa Nijeriya guraben Hajji. Sai dai, an ƙi amincewa da dukkan buƙatun, wanda ya nuna a fili cewa ba Nijeriya ce ta ƙi karɓar ƙarin guraben ba.















Discussion about this post