Sakon taya murna da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike ga taro na 39 na kungiyar Tarayyar Afrika (AU) ya samu yabo sosai a fadin nahiyar da ma kasa da kasa.
Cikin sakon, Xi Jinping ya sanar cewa, a ranar 1 ga watan Mayun 2026, Sin za ta fara aiwatar da manufar soke haraji ga kasashen Afrika 53 dake da huldar diplomasiyya da ita. Ya kuma bayyana cewa kasarsa na kokarin inganta hanyar shigar kayayyakin da ba sa bukatar biyan haraji.
Jami’ai a Afrika da wakilan MDD sun ce sakon na shugaba Xi, ya nuna goyon baya mai karfi ga ‘yancin ci gaban Afrika.
Da yake tsokaci, Henry Okello Oryem, ministan harkokin wajen Uganda, ya yi maraba da matakin shugaba Xi na kara yawan cinikayya tsakanin kasarsa da nahiyar Afrika. Ya ce soke haraji kan kayayyakin Afrika dake shiga Sin, kyakkyawar dama ce ta musamman a garesu ta kara yawan kayayyakin da ake fitarwa zuwa kasar Sin.
Su ma kamfanoni da dama na Afrika dake son shiga kasuwar Sin, sun bayyana sabbin matakan kamar na soke haraji, a matsayin wadanda za su samar musu da sabbin damarmakin fadada cinikayya da Sin da inganta wa kayayyakinsu karfin takara.
Da yake jawabi ga manema labarai a gefen taro na 39 na AU, sakatare janar na MDD Antonio Guterrs, ya yaba da manufar soke harajin ta Sin, yana mai kira ga manyan kasashe da dukkan kasashe masu karfin tattalin arziki su yi koyi da ita. (FMM)















Discussion about this post