Ofishin jakadancin kasar Sin a kasar Namibia, ya yi wa wakilan kafofin watsa labarai, da kwararru karin haske game da manufar Sin ta janye daukacin haraji kan hajojin kasashen Afirka da ake shigarwa kasuwar kasar Sin.
Ofishin ya ce wannan manufa za ta samar da sabbin damammaki ga Namibia, tare da mara baya ga aikin bunkasa masana’antun kasar.Kazalika, ofishin jakadancin na kasar Sin a Namibia, ya ce kayayyaki irin su naman shanu da na awaki, da sauran albarkatun ruwa da kasar ke fitarwa, da kayan marmari irinsu inabi, da blueberries, za su ci gajiyar janye harajin na Sin, kuma hakan zai samar da muhimmin zarafi na fadada cinikayya tare da Sin, da zarar ka’idoji da tsare-tsaren fitar da hajojin sun kammala.
Bayan taron fadakarwar, wani mai nazarin tattalin arziki dan kasar Namibia Josef Sheehama, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua, cewa manufar kawar da harajin za ta samar da muhimmin sauyi ga Namibia, da ma daukacin kasashen Afirka baki daya. Sheehama ya ce “Na yi imanin cewa za mu fadada hada-hadar fitar da hajojinmu, kuma hakan dama ce ga Namibia da Afirka baki daya.”
A nasa bangare kuwa, dan jarida Philip Josef, ya ce manufar tana da babbar fa’ida, musamman ga kanana da matsakaitan kamfanoni, da matasa masu aiwatar da sana’o’i, duba da cewa manufar za ta saukaka matsi kan kasuwanci da kyautata damar shiga kasuwannin kasar Sin.
Philip Josef, ya kara da cewa kamata ya yi Namibia ta yi nazari sama da kan gajiyar nan take, ta lura da hanyoyin cimma gajiya ta dogon lokaci. (Saminu Alhassan)














Discussion about this post