ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wuta – Tambuwal 

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
4 years ago
Tambuwal

Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na Jihar Sakkwato ya bayyana cewar akwai kalubale sosai a fannin samar da wutar lantarki a Kasar nan wanda ya zama wajibi idan a na son samun ci-gaba mai ma’ana a dauki kwararan matakai domin shawo kan matsalolin.

Ya ce fannin wuta na bukatar kwararru kuma gogaggun hannaye wadanda suke jajirtattu ta hanyar yin aiki da gaske domin shawo kan tarin manyan kalubalen da fannin ya jima yana fuskanta.
Ya ce Nijeriya za ta iya samun ci-gaba ne kadai a matsayin Kasa idan ta na da ingantacciyar wutar lantarki.

Ya ce kashe tsohuwar NEPA bai samu cikakkiyar nasara ba, har yanzu akwai kalubale sosai amma kuma za a iya shawo kan su idan Gwamnati da gaske take yi.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Ta’adda Sun Tarwatsa Kauyuka 21 A Sakkwato

Gwamnan ya yi wannan bayanin ne a yayin da ya karbi bakuncin sabon Shugaban Hukumar Gudanarwar Kamfanin Wutar Lantarki na KAEDCO, Alhaji Abbas Muhammad Jega a Fadar Gwamnatin Sakkwato.
“Kasashe da dama sun yi, me zai hana mu ma mu yi? Ba za mu samu nasarar cika alkawulan mu ba, ba za mu gano damar da muke da ita ba idan ba mu gyara fannin wuta ba.” Ya bayyana.

Ya ce duk fannonin ci-gaba mafi yawa sun dogara ne ga samun wuta wanda a kan hakan ne ya ce Gwamnatinsa ta na goyon bayan bunkasa fannin wutar lantarki wanda a bisa ga wannan ne Gwamnatinsa ta kashe makuddan kudade wajen samar da na’urorin taransifoma da daga darajar layukan wuta a fadin Jihar.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnan ya bukaci Kamfanin da su rika amfani da tsarin lissafin kudin wutar da aka ci maimakon hasashe ba tare da lissafi ba.Ya ce ta hanyar sanya na’urar mita, hasashen kudin wuta da ake yi zai ragu sosai, wanda hakan zai sa a samu gagarumar nasara a kokarin da ake yi na bunkasa fannin samar da wuta.

Tambuwal wanda ya ce yin amfani da tsarin biyan wutar da aka sha, shine mafi dacewa kamar yadda kamfanonin sadarwa ke yi wanda jama’a ke jin dadin tsarin, don haka me zai hana a yi shi a fannin wuta?” Gwamnan ya tambaya.

Ya ce yin hakan zai zama alfanu ga kamfanin domin za a gano kwastomomi na kwarai wadanda ke biyan wuta, haka ma wadanda ke biyan wuta za su gamsu kuma su ga alfanun biyan kudinsu kuma za rika cajinsu yadda ya kamata.

A jawabinsa Abbas Jega ya bayar da tabbacin cewar tattaunawar Kamfanin da Gwamnatin Jihar Sakkwato da jin bukatocin kwastomomin su ya karfafa fahimtar juna da samar da sakamako mai kyau a kakkarfan kamfani da samun wuta a kodayaushe a Jihar.

  • https://leadership.ng/tambuwal-rallies-north-west-businessmen-for-atiku/

Tambuwal, ya kuma bayyana nauyin matsalolin da aka gabatar tare da bayar da tabbacin za su kara tashi tsaye wajen magance matsalolin tare da kara inganta bayar da hasken wuta da rage korafe- korafen jama’a.

Tambuwal
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    A Yayin Da Babban Bankin Ƙasa (CBN) Ke Yaƙi Da Laifukan Intanet
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Halin Da Matsalar Tsaro Ta Jefa ‘Yan Gudun Hijira A Arerwacin Nijeriya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga Faruku Yabo
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dan-Iya Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan ADC A Sakkwato

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Saudiyya Ta Kama Mutumin Da Ya Yi Umrah Saboda Sarauniyar Ingila

Saudiyya Ta Kama Mutumin Da Ya Yi Umrah Saboda Sarauniyar Ingila

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.