ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wuta – Tambuwal 

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
4 years ago
Tambuwal

Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na Jihar Sakkwato ya bayyana cewar akwai kalubale sosai a fannin samar da wutar lantarki a Kasar nan wanda ya zama wajibi idan a na son samun ci-gaba mai ma’ana a dauki kwararan matakai domin shawo kan matsalolin.

Ya ce fannin wuta na bukatar kwararru kuma gogaggun hannaye wadanda suke jajirtattu ta hanyar yin aiki da gaske domin shawo kan tarin manyan kalubalen da fannin ya jima yana fuskanta.
Ya ce Nijeriya za ta iya samun ci-gaba ne kadai a matsayin Kasa idan ta na da ingantacciyar wutar lantarki.

Ya ce kashe tsohuwar NEPA bai samu cikakkiyar nasara ba, har yanzu akwai kalubale sosai amma kuma za a iya shawo kan su idan Gwamnati da gaske take yi.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Ta’adda Sun Tarwatsa Kauyuka 21 A Sakkwato

Gwamnan ya yi wannan bayanin ne a yayin da ya karbi bakuncin sabon Shugaban Hukumar Gudanarwar Kamfanin Wutar Lantarki na KAEDCO, Alhaji Abbas Muhammad Jega a Fadar Gwamnatin Sakkwato.
“Kasashe da dama sun yi, me zai hana mu ma mu yi? Ba za mu samu nasarar cika alkawulan mu ba, ba za mu gano damar da muke da ita ba idan ba mu gyara fannin wuta ba.” Ya bayyana.

Ya ce duk fannonin ci-gaba mafi yawa sun dogara ne ga samun wuta wanda a kan hakan ne ya ce Gwamnatinsa ta na goyon bayan bunkasa fannin wutar lantarki wanda a bisa ga wannan ne Gwamnatinsa ta kashe makuddan kudade wajen samar da na’urorin taransifoma da daga darajar layukan wuta a fadin Jihar.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnan ya bukaci Kamfanin da su rika amfani da tsarin lissafin kudin wutar da aka ci maimakon hasashe ba tare da lissafi ba.Ya ce ta hanyar sanya na’urar mita, hasashen kudin wuta da ake yi zai ragu sosai, wanda hakan zai sa a samu gagarumar nasara a kokarin da ake yi na bunkasa fannin samar da wuta.

Tambuwal wanda ya ce yin amfani da tsarin biyan wutar da aka sha, shine mafi dacewa kamar yadda kamfanonin sadarwa ke yi wanda jama’a ke jin dadin tsarin, don haka me zai hana a yi shi a fannin wuta?” Gwamnan ya tambaya.

Ya ce yin hakan zai zama alfanu ga kamfanin domin za a gano kwastomomi na kwarai wadanda ke biyan wuta, haka ma wadanda ke biyan wuta za su gamsu kuma su ga alfanun biyan kudinsu kuma za rika cajinsu yadda ya kamata.

A jawabinsa Abbas Jega ya bayar da tabbacin cewar tattaunawar Kamfanin da Gwamnatin Jihar Sakkwato da jin bukatocin kwastomomin su ya karfafa fahimtar juna da samar da sakamako mai kyau a kakkarfan kamfani da samun wuta a kodayaushe a Jihar.

  • https://leadership.ng/tambuwal-rallies-north-west-businessmen-for-atiku/

Tambuwal, ya kuma bayyana nauyin matsalolin da aka gabatar tare da bayar da tabbacin za su kara tashi tsaye wajen magance matsalolin tare da kara inganta bayar da hasken wuta da rage korafe- korafen jama’a.

Tambuwal
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dimokuradiyyar Nijeriya A Shekara 27:Ba Yabo Ba Fallasa
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Wamakko Ya Koka Kan Taɓarɓarewar Sha’anin Tsaro

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Saudiyya Ta Kama Mutumin Da Ya Yi Umrah Saboda Sarauniyar Ingila

Saudiyya Ta Kama Mutumin Da Ya Yi Umrah Saboda Sarauniyar Ingila

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.