ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nutsuwa Da Dattakun Annabi Muhammadu (SAW)

by Sulaiman and Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
3 years ago
Annabi

Annabi (SAW), ya raba ranarsa gida Uku: Na farko – Ibada; na biyu – Iyalinsa, na karshe – na kanshi ne. Sannan kuma sai ya sake raba kason kansa gida biyu, na farko ya bai wa kansa, na biyu ya bai wa Jama’arsa.

Manzon Allah (SAW) ya kasance yana neman taimakon kebantattunsa daga gama-gari, inda yake cewa, ku wadanda kuke tare da ni, ku dinga isar min da bukatar wadanda ba za su iya isowa gare ni ba da bukatarsu. Yadda abun yake shi ne, duk wanda ya isar da bukatar wani wanda ba zai iya isar da ita ba, Allah Ubangiji zai amintar da shi ranar tsoro babba (Ranar Alkiyama). Misali, Mutum ba zai iya isar da gaskiyarsa a kotu ba, to Lauya ya isar masa. Sabida, wani in ya je kotu da gaskiyarsa sai ya gigice ya kasa bayyana ta, to Lauya mai gaskiya ya isar masa.

  • Budi Da Cikar Ni’imar Allah Ga Annabi Muhammadu (SAW)

An karba daga Hassan, Dan Sayyadina Ali (RA) yana cewa, Manzon Allah (SAW) ya kasance, ba ya rike wani mutum daya da kagen wani. Don wani ya kitsa karya a kan wani mutum, Annabi (SAW) ba ya kama mutum da ita har sai ya yi bincike a kanta. Sannan kuma bai gasgata maganar wani a kan wani har sai ya yi bincike gaskiya ta bayyana.

ADVERTISEMENT

Abu Ja’afaril Dabri ya fitar da Hadisi, daga Sayyadina Ali daga Annabi (SAW) yana cewa, “ban taba himmar aikata wani abu daga abin da ‘yan jahilyya suke aikatawa da shi ba sai sau biyu, amma dukka guda biyun sai Allah ya tsare ni daga aikatawa, har Allah ya girmama ni da aikensa”. Abubuwa biyun su ne:
Na farko: Wata rana Annabi (SAW) yana kiwo a wajen garin Makkah tare da wani Yaro, sai ya ce wa yaron da za ka kula min da tumakina in shiga cikin garin Makkah ni ma in dan shakata kamar yadda sauran samari suke shiga, sabida kullun muna cikin dajin kiwo, sai yaron ya amince, ni kuma na shirya, har sai da na zo gidan farko na shiga garin Makkah, sai na ji ana buga ganga da algaita sabida wani aure da ake yi, sai na zauna ina kallo, sai Ubangiji ya yi rufi a kunnena na daina jin komai (ya yi bacci), ban farka ba har sai da hasken rana ya tashe ni. Ban kewaya a gari ba, ga shi na bar tumakina.

Na biyu: shi ma irin na farko ne, amma Allah ya kawo wani abu shi ma na yi bacci. Daga nan, na ce ba zan kara zuwa ba tun da ban da rabo cikin irin wadannan abubuwan.
Shi Mumini duk lokacin da ya yi yunkurin aikata wani abu da shari’ar musulunci ba ta yarda da shi ba, sai Allah ya tona asiri amma wanda ba Mumini ba sai ya dade yana aikata barna Allah bai tona masa asiri ba sabida Allah babu ruwanshi da shi.

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

Sabon Darasi da zai yi Magana kan Nutsuwa da Mutuntaka (Daddaku) ta Annabi (SAW).
Game da Nutsuwar Manzon Allah (SAW) da Kawaicinsa da kuma rashin gaggawa (yin abu a sannu-sannu) da mutuntakarsa da kyakkyawar shiryarwarsa, Umar bin Abdulaziz bin Huwair ya ce, ya ji Harisata dan Zaidu yana cewa, Annabi (SAW) ya kasance mafi nutsuwar mutane a mazauninsa, ba za ka ji wani abu ya fito daga cikin Annabi (SAW) ba kamar Kaki, Ballan Kashi, Tusa da dai sauransu in yana zaune cikin Jama’a amma in ya koma gida yakan sakin jikinsa.

Abu Sa’idil Kuduri ya ruwaito hadisi yana cewa, Manzon Allah (SAW) ya kasance idan ya zauna a mazauni sai ya yi ihkaba’i (wani irin tsarin zama ne da Larabawa ke kulle gabobinsu da gobobinsu, sabida mutane ne a Sahara, ba su da Bango na jingina), Manzon Allah (SAW) ya kasance mafi yawancin tsarin zamansa, Ihkaba’i.

An karba Hadisi daga Jabir dan Samurata, ya ce Manzon Allah (SAW) yana harde Kafarsa wurin zama, da yawa yake zaman Kurfasa’u. Manzon Allah (SAW) ya kasance mai yawan shiru in ba karatu yake yi ba, da yawa yake kauda kai ga wanda ya yi magana wacce ba ta dace ba a tsakiyar zance. Dariyar Annabi (SAW) ta kasance murmushi ce, wani lokacin yakan yi dariya har Turamen hakoransa su bayyana, Kalamansa a rarrabe suke – Hikima ce cikakkiya ba cakudin magana ba, Mai yawan Zikiri ne ba ya magana sai in ta dace, dariyar Sahabbansa a gabansa murmushi ce don koyi da kuma girmamawa a gareshi.

Mazaunin Manzon Allah (SAW), mazauni ne na karatu da hakuri da kunya da alkhairi da amana, ba a daga muryoyi a mazauninsa wacce za ta zama ta rashin ladabi, ba a keta alfarmar mai alfarma a mazauninsa, idan yana magana da sahabbansa ka ce tsuntsu ne a kan kafadunsu sabida nutsuwa.

Yana daga cikin abubuwan da aka ruwaito cewa, Manzon Allah (SAW) in yana tafiya, tafiyarsa kamar ciccirawa yake yi da kuzari amma a natse, in yana tafiya, kamar yana saukowa daga tudu, sahabbai sai sun hada da gudu shi kuma tafiya dai-dai yake yi. Don haka, sahabbai ke cewa, suna zaton ana nade masa kasa ne wurin tafiya.

A wani hadisi kuma, ya zo cewa, idan Annabi (SAW) yana tafiya, tafiya yake yi baki daya ba rangaji ko rangwada ba. Ana gane Annabi a tafiya cewa, ba ya tafiyar gajiyayyu ko tafiyar kasalallu.

Abdullahi bin Mas’ud ya ce, mafi kyawun shiryarwa dai, ita ce shiryarwar Annabi Muhammadu (SAW).

An karba daga Jabiru, Allah ya yarda da shi ya ce, akwai Fasaha (rarrabe magana) a cikin maganar Annabi Muhammad (SAW).
Dan Abi Halata yake fada cewa, Shirun Annabi (SAW) ya kasu gida Hudu:
Akwai shirun hakuri – wani ya yi wauta, yana da ikon da zai sa a sare masa kai amma sai ya yi shiru don kar ya fada wata magana ta zama hukunci kuma ga masu zartaswa a kusa.

Akwai shirun taka-tsan-tsan – kar Annabi (SAW) ya yi magana ta zama hatsari sabida irin wurin da ake, da irin mutanen da ake cikinsu (mutanen za su iya daukar sirrin ko ba za su iya ba).

Akwai shiru na cikin girmansa – akwai maganar da ba ta kai Annabi (SAW) ya tanka ba, wani in ka mayar masa da magana ka girmama shi.

Akwai shirun tunani cikin Allah – Manzon Allah (SAW) kullum cikin tafakkurin Ubangiji yake, don haka yake Istigfari, in an kai mataki na gaba sai a fahimta. Annabi (SAW) kullun ci gaba yake da tafiya a Hadarar Ubangijinsa.
Sayyada A’isha (RA) ta ce, Annabi (SAW) ya kasance yana zantar da zance, da mai kirgawa zai kirga kalmomin zancen, da sai a ga kalmomin da Annabi ya yi amfani da su sabida rarrabe zance da rashin sauri a ciki.

Wata rana Abi Hurairah yana bayar da Karatu, sai ya ji Sayyada A’isha tana Sallah a bayanshi kuma kamar tana sauri ta idar, sai Abi Hurairah ya fahimci sabida shi take sauri, sai ya yi sauri ya wuce, bayan ta yi sallama, ta tambaya ina yake? Aka ce, ya wuce, sai ta ce, ba karyata shi zan yi ba amma yadda yake karatu da sauri-sauri ba haka Annabi (SAW) yake yi ba.

Manzon Allah ya kasance yana son Turare da kamshi mai dadi, kuma yana amfani da duk wani abu mai kamshi, yana kwadaitarwa akan Turare, yana cewa “a cikin duniyar nan taku, an soyar min da Mata in auresu don halas sai kuma Turare, an sanya sanyin idanuna a cikin Sallah, ba na nutsuwa sai na tayar da Sallah.”

Annabi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Annabi
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ posts Bio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)

MASU ALAKA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Dausayin Musulunci

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

May 29, 2026
Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
Dausayin Musulunci

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

May 22, 2026
Annabi
Dausayin Musulunci

Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci

May 15, 2026
Next Post
Firimiya Lig: Wasanni Uku Da Za Su Fi Daukar Hankalin Masu Kallo A Wannan Makon

Firimiya Lig: Wasanni Uku Da Za Su Fi Daukar Hankalin Masu Kallo A Wannan Makon

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.