ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NWC Ne Kadai Ke Da Ikon Dakatar Da Ganduje Daga Shugabancin APC – Abdulkarim Kana

by Sadiq
2 years ago
Ganduje

Mai bai wa jam’iyyar APC shawara kan harkokin shari’a, Abdulkarim Kana, ya ce kwamitin ayyuka na jam’iyyar na kasa (NWC) ne, kadai ke da alhakin dakatar da shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Umar Ganduje.

Kana, ya bayyana haka ne yayin hira a shirin siyasa na gidan talabijin na Channels a ranar Litinin.

  • Karancin Wuta: Nijeriya Za Ta Daina Sayar Wa Kasashen Ketare Wutar Lantarki 
  • Matashiya Ta Kashe Kanta Ta Hanyar Shan Maganin Ƙwari A Delta

Ya yi wannan martani ne kan dakatarwar da wasu shugabannin jami’yyar APC a mazaɓar Ganduje da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano, suka yi wa shugaban jam’iyyar na ƙasa.

ADVERTISEMENT

Shugabannin jam’iyyar a mazaɓar sun dakatar da Ganduje, bisa zargin cin hanci da rashawa, a lokacin da yake gwamnan Kano.

Sai dai shugabancin jam’iyyar APC na Jihar Kano, ya soke dakatarwar tare da korar waɗanda suka dakatar shi daga jam’iyyar.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Wata babbar kotun tarayya da ke Kano, ta jaddada hukuncin dakatarwar da aka yi wa Ganduje na wucin gadi, zuwa lokacin da za ta kammala shari’a kan zarge-zargen da ake masa.

Alkalin babbar kotun da ke Kano, wanda tun farko ya tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje, ya janye dakatarwar da kotun ta yi wa tsohon gwamnan na Kano a matsayin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa.

Da yake magana a ranar Litinin, Kana ya ce babu wata ƙungiya a jam’iyyar da ke da hurumin dakatar da kowane ɗan jam’iyyar face kwamitin ayyuka na jami’yyar na ƙasa.

A cewarsa kamar yadda kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya tanadar, dole ne a bi wasu matakai kafin zartar da irin wancan hukunci da aka ɗauka a kan Ganduje.

“Duk waɗannan hanyoyi dole ne a kare su kafin zartar da irin wannan hukunci idan an kammala bincike, babu wata ƙungiya a APC da ke da hurumin dakatar da duk wani ɗan jam’iyya da ake bincike a kansa sai kwamitin ayyuka na ƙasa,” in ji shi.

Kana, ya ce waɗanda suka dakatar da Ganduje babu wanda ya san da zamansu a jam’iyyar.

Ya ce: “…Na san wasu ɗaiɗaikun mutane, su ba shugabannin mazaɓar Ganduje ba ne, kuma ba shugabannin unguwanni ba ne. Tun da farko, lokacin da waɗannan bayanai suka bayyana a gare mu, abu na farko da muka yi shi ne bincike kuma muna da hanyar da za mu tabbatar da ko akwai waɗancan zarge-zarge.

“Wannan babban zargi ne, cewa wata ƙungiya a jam’iyyar za ta ɗauki wannan mataki. Mun gudanar da bincikenmu, kuma ba a ɗauki lokaci mai tsawo ba muka gano waɗanda suka ce sun dakatar da shugaban jam’iyyar na ƙasa, ba ‘ya’yan jami’yyar ba ne a mazaɓar Ganduje ba.

“Ofishina bai tsaya karɓar rahotanni daga ɗaiɗaikun mutane dangane da sahihancin wannan zargi ba, mun gayyaci kwamitin ayyuka na jiha tare da na mazaɓa zuwa Abuja domin tattaunawa da su, kuma na dage sai sun zo da katin shaida da kuma katin zaɓensu.

“Lokacin da suka zo da katin shaidarsu, sai muka gano cewa waɗanda suka bayyana a talabijin kan wancan zarge-zarge ba su ne a jikin katin shaidar ba, wannan lamari yana da girman gaske.

“Hakan ne ya sanya ba mu ɓata lokaci ba wajen sanya jami’an tsaro cikin lamarin domin gudanar da bincike kan dalilin da ya sa waɗannan mutane za su yi wannan zarge-zarge, ‘yan damfara ne, abin da suke yi kenan. Kuma mun karɓi koke daga shugabannin mazaɓar na gaskiya wanda muka aike wa ‘yan sanda, yanzu maganar tana gaban ‘yan sanda domin gudanar da bincike.”

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Sabon Harajin Tsaron Yanar Gizo Bai Shafi Hada-hadar Kudi 16 Ba – CBN

Sabon Harajin Tsaron Yanar Gizo Bai Shafi Hada-hadar Kudi 16 Ba - CBN

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.