• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NWC Ne Kadai Ke Da Ikon Dakatar Da Ganduje Daga Shugabancin APC – Abdulkarim Kana

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Ganduje Ya Zargi ‘Yan Siyasa Da Hannu A Haddasa Rikice-rikicen Zabe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai bai wa jam’iyyar APC shawara kan harkokin shari’a, Abdulkarim Kana, ya ce kwamitin ayyuka na jam’iyyar na kasa (NWC) ne, kadai ke da alhakin dakatar da shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Umar Ganduje.

Kana, ya bayyana haka ne yayin hira a shirin siyasa na gidan talabijin na Channels a ranar Litinin.

  • Karancin Wuta: Nijeriya Za Ta Daina Sayar Wa Kasashen Ketare Wutar Lantarki 
  • Matashiya Ta Kashe Kanta Ta Hanyar Shan Maganin Ƙwari A Delta

Ya yi wannan martani ne kan dakatarwar da wasu shugabannin jami’yyar APC a mazaɓar Ganduje da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano, suka yi wa shugaban jam’iyyar na ƙasa.

Shugabannin jam’iyyar a mazaɓar sun dakatar da Ganduje, bisa zargin cin hanci da rashawa, a lokacin da yake gwamnan Kano.

Sai dai shugabancin jam’iyyar APC na Jihar Kano, ya soke dakatarwar tare da korar waɗanda suka dakatar shi daga jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Wata babbar kotun tarayya da ke Kano, ta jaddada hukuncin dakatarwar da aka yi wa Ganduje na wucin gadi, zuwa lokacin da za ta kammala shari’a kan zarge-zargen da ake masa.

Alkalin babbar kotun da ke Kano, wanda tun farko ya tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje, ya janye dakatarwar da kotun ta yi wa tsohon gwamnan na Kano a matsayin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa.

Da yake magana a ranar Litinin, Kana ya ce babu wata ƙungiya a jam’iyyar da ke da hurumin dakatar da kowane ɗan jam’iyyar face kwamitin ayyuka na jami’yyar na ƙasa.

A cewarsa kamar yadda kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya tanadar, dole ne a bi wasu matakai kafin zartar da irin wancan hukunci da aka ɗauka a kan Ganduje.

“Duk waɗannan hanyoyi dole ne a kare su kafin zartar da irin wannan hukunci idan an kammala bincike, babu wata ƙungiya a APC da ke da hurumin dakatar da duk wani ɗan jam’iyya da ake bincike a kansa sai kwamitin ayyuka na ƙasa,” in ji shi.

Kana, ya ce waɗanda suka dakatar da Ganduje babu wanda ya san da zamansu a jam’iyyar.

Ya ce: “…Na san wasu ɗaiɗaikun mutane, su ba shugabannin mazaɓar Ganduje ba ne, kuma ba shugabannin unguwanni ba ne. Tun da farko, lokacin da waɗannan bayanai suka bayyana a gare mu, abu na farko da muka yi shi ne bincike kuma muna da hanyar da za mu tabbatar da ko akwai waɗancan zarge-zarge.

“Wannan babban zargi ne, cewa wata ƙungiya a jam’iyyar za ta ɗauki wannan mataki. Mun gudanar da bincikenmu, kuma ba a ɗauki lokaci mai tsawo ba muka gano waɗanda suka ce sun dakatar da shugaban jam’iyyar na ƙasa, ba ‘ya’yan jami’yyar ba ne a mazaɓar Ganduje ba.

“Ofishina bai tsaya karɓar rahotanni daga ɗaiɗaikun mutane dangane da sahihancin wannan zargi ba, mun gayyaci kwamitin ayyuka na jiha tare da na mazaɓa zuwa Abuja domin tattaunawa da su, kuma na dage sai sun zo da katin shaida da kuma katin zaɓensu.

“Lokacin da suka zo da katin shaidarsu, sai muka gano cewa waɗanda suka bayyana a talabijin kan wancan zarge-zarge ba su ne a jikin katin shaidar ba, wannan lamari yana da girman gaske.

“Hakan ne ya sanya ba mu ɓata lokaci ba wajen sanya jami’an tsaro cikin lamarin domin gudanar da bincike kan dalilin da ya sa waɗannan mutane za su yi wannan zarge-zarge, ‘yan damfara ne, abin da suke yi kenan. Kuma mun karɓi koke daga shugabannin mazaɓar na gaskiya wanda muka aike wa ‘yan sanda, yanzu maganar tana gaban ‘yan sanda domin gudanar da bincike.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCCin Hanci Da RashawaGandujekanoNWCShugabancin APCZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karancin Wuta: Nijeriya Za Ta Daina Sayar Wa Kasashen Ketare Wutar Lantarki 

Next Post

Sabon Harajin Tsaron Yanar Gizo Bai Shafi Hada-hadar Kudi 16 Ba – CBN

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

4 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

5 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

6 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

9 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

12 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

13 hours ago
Next Post
Sabon Harajin Tsaron Yanar Gizo Bai Shafi Hada-hadar Kudi 16 Ba – CBN

Sabon Harajin Tsaron Yanar Gizo Bai Shafi Hada-hadar Kudi 16 Ba - CBN

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.