A yau Talata 12 ga watan Mayu, Peng Liyuan, uwargidan shugaban kasar Sin Xi Jinping, wadda kuma ita ce jakadiya ta musamman ta hukumar bunkasa ilimi da kimiyya da fasaha da al’adu ta MDD, watau UNESCO kan bunkasa ilimin mata yara da manya, ta gana da darakta janar na UNESCO, Khaled El-Enany, a birnin Beijing.
Peng Liyuan ta taya Khaled El-Enany murnar zabensa a matsayin darakta janar na UNESCO, sannan ta yaba da muhimmiyar rawar da hukumar ke takawa wajen karfafa ilimin mata yara da manya a duniya.
Peng Liyuan ta bayyana nasarorin da Sin ta samu wajen bunkasa ilimin mata yara da manya, tare da shan alwashin ci gaba da sauke nauyin da ke wuyanta a matsayin jakadiya ta musamman da kuma karfafa hadin gwiwa da UNESCO.
A nasa bangaren, Khaled El-Enany ya yaba sosai da gudummawar da Peng Liyuan ta bayar ga harkar ilimin mata yara da manya a duniya tun bayan da ta zama jakadiya ta musamman.
Ya kuma nuna godiyar UNESCO da irin muhimmiyar gudummawar da kasar Sin ke bayarwa. Haka kuma ya bayyana aniyarsa ta kara zurfafa mu’amala da hadin gwiwa da kasar Sin domin samar da sabbin ci gaba a harkar ilimin mata yara da manya a duniya. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post