ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Ga Limamai 40 A Zamfara

by Sulaiman
7 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya raba motoci ga limamai 40 na masallatan Juma’a a faɗin jihar, a wani mataki da gwamnatin ta ce na daga cikin ƙoƙarinta na tallafa wa shugabannin addini domin sauƙaƙa musu gudanar da ayyukansu na wa’azi da hidima ga al’umma.

 

Da yake jawabi yayin rabon motocin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa manufar shirin ita ce inganta zirga-zirgar limaman da kuma ƙara musu damar kai saƙonnin addini da nasiha zuwa sassa daban-daban na al’umma.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Jihar Gombe Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar New Zealand Kan Kiwon Dabbobi
  • Ramadan: Zulum Ya Raba Wa Magidanta 300,000 Kayan Abinci A Borno

Ya ce, Zamfara jiha ce da aka gina bisa tubalan addinin Musulunci, inda limamai ke taka muhimmiyar rawa wajen shiryar da jama’a a kan tafarkin gaskiya da adalci a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A cewarsa, kula da jin daɗin shugabannin addini na daga cikin abubuwan da gwamnatinsa ta bai wa muhimmanci. Ya bayyana cewa baya ga gina masallatai da gidaje ga limamai, gwamnati ta ga dacewar samar musu da hanyoyin sufuri domin sauƙaƙa musu zirga-zirga, musamman a ayyukan wa’azi da hulɗa da al’umma.

 

Gwamnan ya ce, an zabo limamai 40 a wannan mataki na farko, yana mai jaddada cewa shirin zai ci gaba a nan gaba domin faɗaɗa tallafin zuwa wasu limamai. Ya kuma roƙi malaman da su ci gaba da yi wa jihar Zamfara da Nijeriya baki daya addu’ar zaman lafiya mai ɗorewa da kwanciyar hankali.

 

Tun da farko, Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Addini, Sheikh Bello Almufty, ya yabawa Gwamna Lawal, yana mai cewa jagora ne mai gaskiya da kishin ci gaban kowa da kowa. Ya ce gwamnatin ta kawo sauyi mai ma’ana a rayuwar shugabannin addini ta hanyar inganta walwalarsu da alawus-alawus ɗinsu.

 

A madadin limaman da suka amfana, Sheikh Atiku Zawiyya ya nuna godiya ga gwamnan bisa wannan tallafi, yana mai cewa motocin za su taimaka wajen ƙara ƙarfin ayyukan wa’azi da hidima ga jama’a. Ya yi addu’ar Allah ya ƙara bai wa gwamnan ikon ci gaba da ayyukan alheri, yana mai cewa irin wannan kyauta na buƙatar lada daga Allah.

 

Limaman da suka amfana sun kuma sha alwashin ci gaba da yaɗa saƙon zaman lafiya, haɗin kai da kyawawan ɗabi’u a cikin al’ummominsu.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
jam'iyyu

Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.