ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Ga Limamai 40 A Zamfara

by Sulaiman
4 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya raba motoci ga limamai 40 na masallatan Juma’a a faɗin jihar, a wani mataki da gwamnatin ta ce na daga cikin ƙoƙarinta na tallafa wa shugabannin addini domin sauƙaƙa musu gudanar da ayyukansu na wa’azi da hidima ga al’umma.

 

Da yake jawabi yayin rabon motocin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa manufar shirin ita ce inganta zirga-zirgar limaman da kuma ƙara musu damar kai saƙonnin addini da nasiha zuwa sassa daban-daban na al’umma.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnatin Jihar Gombe Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar New Zealand Kan Kiwon Dabbobi
  • Ramadan: Zulum Ya Raba Wa Magidanta 300,000 Kayan Abinci A Borno

Ya ce, Zamfara jiha ce da aka gina bisa tubalan addinin Musulunci, inda limamai ke taka muhimmiyar rawa wajen shiryar da jama’a a kan tafarkin gaskiya da adalci a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

A cewarsa, kula da jin daɗin shugabannin addini na daga cikin abubuwan da gwamnatinsa ta bai wa muhimmanci. Ya bayyana cewa baya ga gina masallatai da gidaje ga limamai, gwamnati ta ga dacewar samar musu da hanyoyin sufuri domin sauƙaƙa musu zirga-zirga, musamman a ayyukan wa’azi da hulɗa da al’umma.

 

Gwamnan ya ce, an zabo limamai 40 a wannan mataki na farko, yana mai jaddada cewa shirin zai ci gaba a nan gaba domin faɗaɗa tallafin zuwa wasu limamai. Ya kuma roƙi malaman da su ci gaba da yi wa jihar Zamfara da Nijeriya baki daya addu’ar zaman lafiya mai ɗorewa da kwanciyar hankali.

 

Tun da farko, Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Addini, Sheikh Bello Almufty, ya yabawa Gwamna Lawal, yana mai cewa jagora ne mai gaskiya da kishin ci gaban kowa da kowa. Ya ce gwamnatin ta kawo sauyi mai ma’ana a rayuwar shugabannin addini ta hanyar inganta walwalarsu da alawus-alawus ɗinsu.

 

A madadin limaman da suka amfana, Sheikh Atiku Zawiyya ya nuna godiya ga gwamnan bisa wannan tallafi, yana mai cewa motocin za su taimaka wajen ƙara ƙarfin ayyukan wa’azi da hidima ga jama’a. Ya yi addu’ar Allah ya ƙara bai wa gwamnan ikon ci gaba da ayyukan alheri, yana mai cewa irin wannan kyauta na buƙatar lada daga Allah.

 

Limaman da suka amfana sun kuma sha alwashin ci gaba da yaɗa saƙon zaman lafiya, haɗin kai da kyawawan ɗabi’u a cikin al’ummominsu.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
Next Post
jam'iyyu

Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.