ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar New Zealand Kan Kiwon Dabbobi

by Abubakar Abba and Sulaiman
5 months ago
gombe

Gwamnatin Jihar Gombe da hukumar bunkasa fannin kiwon dabbobi na zamani (LIC) da ke kasar New Zealand, sun rattaba hannun yarjejeniyar bunkasa fannin kiwon dabbobi na zamani tare da kuma kara karfafa jurewar kiwo na kowane irin yanayi da kuma kara samar da wata sabuwar damar haBaka tattalin arzikin da ke fannin na jihar.

Sun kulla wannan yarjejeniyar ce, biyo bayan wata ziyara ta kwana biyu da Gwaman Jihar Muhammadu Inuwa Yahaya, ya jagoranci wata tawaga zuwa hukumar, inda ziyarar ta bayar da damar kulla wannan yarjejeniya.

  • Amurka Ta Kwace Kadarorin ‘Yan Nijeriya 8 Masu Alaka Da Boko Haram
  • Kisan Ƙare Dangi: Sojojin Amurka Sun Fara Aikin Samar Da Tsaro A Nijeriya

Isma’ila Uba Misilli, Darakta Janar na yada labaran gwamnan ya bayyana hakan a cikin sanarwar da ya fitar, inda sanarwar ta ce; a karkashin wannan yarjejeniya, Bangarorin biyu za su kaddamar da gudanar shirin bincken hadaka a tsakaninsu, wacce za a sanya jami’ar Jihar Gombe, domin gudanar da binciken, musamman kan yadda za a fito da damar jinsin dabbobi tare da kuma gabatar da sabon tsarin samar da Madarar Shanu da namansu.

ADVERTISEMENT

Gwamna Yahaya, a jawabinsa a wajen rattaba hannun yarjejeniyar ya danganta hadakar a matsayin mai matukar muhimmanci da kuma girma, musamman domin a kara bunkasa kokarin da gwamnatin jihar ke ci gaba da yi na haBaka fannin kiwon dabbobi.

Ya bayyana cewa, wannan shirin ya yi daidai da irin kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi, na saita fannin kiwon dabbobi na kasar, ta hanyar amfani da ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi ta tarayya.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Shi kuwa a nasa jawabin, babban ministan ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi, Idi Mukhtar Maiha, ya yaba da wannan yarjejeniyar, wanda ya ce; ta zo daidai da irin kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba yi, na kara bunkasa fannin kiwon dabbobi na kasar, musamman gannin yadda gwamnatin ke da yakinin cewa; yin kiwon dabbobin na zamani, zai kara haBaka fannin a kasar nan.

Shi ma a nasa jawabin, a madadin hukumar Manajan Bunkasa Samar da Madarar Shanu na kasa da kasa, Jason Schrier, ya yi maraba da kulla wannan yarjejeniyar wadda kuma ya danganta ta a matsayin wani mataki na kara haBaka hadakar kasa da kasa, ta bunkasa fannin kiwon dabbobi.

Ya bayyana cewa, a karkashin wannan yarjejeniyar, hukumar za ta kawo kwararru, inda hakan zai kara taimaka wa masu kiwon dabbobi da ke jihar ta Gombe, har na dogon zango.

An dai kafa wannan hukumar ce a shekarar 1909, wadda kuma ta ke ci gaba da zama kan gaba a fannin yin kiwon dabbobi ta hanyar amfani da fasahar kimiyyar zamani.

Gombe
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
Gombe
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Dakile Harin ISWAP Da Boko Haram A Borno

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.