ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar New Zealand Kan Kiwon Dabbobi

by Abubakar Abba and Sulaiman
4 months ago
gombe

Gwamnatin Jihar Gombe da hukumar bunkasa fannin kiwon dabbobi na zamani (LIC) da ke kasar New Zealand, sun rattaba hannun yarjejeniyar bunkasa fannin kiwon dabbobi na zamani tare da kuma kara karfafa jurewar kiwo na kowane irin yanayi da kuma kara samar da wata sabuwar damar haBaka tattalin arzikin da ke fannin na jihar.

Sun kulla wannan yarjejeniyar ce, biyo bayan wata ziyara ta kwana biyu da Gwaman Jihar Muhammadu Inuwa Yahaya, ya jagoranci wata tawaga zuwa hukumar, inda ziyarar ta bayar da damar kulla wannan yarjejeniya.

  • Amurka Ta Kwace Kadarorin ‘Yan Nijeriya 8 Masu Alaka Da Boko Haram
  • Kisan Ƙare Dangi: Sojojin Amurka Sun Fara Aikin Samar Da Tsaro A Nijeriya

Isma’ila Uba Misilli, Darakta Janar na yada labaran gwamnan ya bayyana hakan a cikin sanarwar da ya fitar, inda sanarwar ta ce; a karkashin wannan yarjejeniya, Bangarorin biyu za su kaddamar da gudanar shirin bincken hadaka a tsakaninsu, wacce za a sanya jami’ar Jihar Gombe, domin gudanar da binciken, musamman kan yadda za a fito da damar jinsin dabbobi tare da kuma gabatar da sabon tsarin samar da Madarar Shanu da namansu.

ADVERTISEMENT

Gwamna Yahaya, a jawabinsa a wajen rattaba hannun yarjejeniyar ya danganta hadakar a matsayin mai matukar muhimmanci da kuma girma, musamman domin a kara bunkasa kokarin da gwamnatin jihar ke ci gaba da yi na haBaka fannin kiwon dabbobi.

Ya bayyana cewa, wannan shirin ya yi daidai da irin kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi, na saita fannin kiwon dabbobi na kasar, ta hanyar amfani da ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi ta tarayya.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Shi kuwa a nasa jawabin, babban ministan ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi, Idi Mukhtar Maiha, ya yaba da wannan yarjejeniyar, wanda ya ce; ta zo daidai da irin kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba yi, na kara bunkasa fannin kiwon dabbobi na kasar, musamman gannin yadda gwamnatin ke da yakinin cewa; yin kiwon dabbobin na zamani, zai kara haBaka fannin a kasar nan.

Shi ma a nasa jawabin, a madadin hukumar Manajan Bunkasa Samar da Madarar Shanu na kasa da kasa, Jason Schrier, ya yi maraba da kulla wannan yarjejeniyar wadda kuma ya danganta ta a matsayin wani mataki na kara haBaka hadakar kasa da kasa, ta bunkasa fannin kiwon dabbobi.

Ya bayyana cewa, a karkashin wannan yarjejeniyar, hukumar za ta kawo kwararru, inda hakan zai kara taimaka wa masu kiwon dabbobi da ke jihar ta Gombe, har na dogon zango.

An dai kafa wannan hukumar ce a shekarar 1909, wadda kuma ta ke ci gaba da zama kan gaba a fannin yin kiwon dabbobi ta hanyar amfani da fasahar kimiyyar zamani.

Gombe
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
Gombe
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Dakile Harin ISWAP Da Boko Haram A Borno

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.