ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar New Zealand Kan Kiwon Dabbobi

by Abubakar Abba and Sulaiman
3 months ago
gombe

Gwamnatin Jihar Gombe da hukumar bunkasa fannin kiwon dabbobi na zamani (LIC) da ke kasar New Zealand, sun rattaba hannun yarjejeniyar bunkasa fannin kiwon dabbobi na zamani tare da kuma kara karfafa jurewar kiwo na kowane irin yanayi da kuma kara samar da wata sabuwar damar haBaka tattalin arzikin da ke fannin na jihar.

Sun kulla wannan yarjejeniyar ce, biyo bayan wata ziyara ta kwana biyu da Gwaman Jihar Muhammadu Inuwa Yahaya, ya jagoranci wata tawaga zuwa hukumar, inda ziyarar ta bayar da damar kulla wannan yarjejeniya.

  • Amurka Ta Kwace Kadarorin ‘Yan Nijeriya 8 Masu Alaka Da Boko Haram
  • Kisan Ƙare Dangi: Sojojin Amurka Sun Fara Aikin Samar Da Tsaro A Nijeriya

Isma’ila Uba Misilli, Darakta Janar na yada labaran gwamnan ya bayyana hakan a cikin sanarwar da ya fitar, inda sanarwar ta ce; a karkashin wannan yarjejeniya, Bangarorin biyu za su kaddamar da gudanar shirin bincken hadaka a tsakaninsu, wacce za a sanya jami’ar Jihar Gombe, domin gudanar da binciken, musamman kan yadda za a fito da damar jinsin dabbobi tare da kuma gabatar da sabon tsarin samar da Madarar Shanu da namansu.

ADVERTISEMENT

Gwamna Yahaya, a jawabinsa a wajen rattaba hannun yarjejeniyar ya danganta hadakar a matsayin mai matukar muhimmanci da kuma girma, musamman domin a kara bunkasa kokarin da gwamnatin jihar ke ci gaba da yi na haBaka fannin kiwon dabbobi.

Ya bayyana cewa, wannan shirin ya yi daidai da irin kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi, na saita fannin kiwon dabbobi na kasar, ta hanyar amfani da ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi ta tarayya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Shi kuwa a nasa jawabin, babban ministan ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi, Idi Mukhtar Maiha, ya yaba da wannan yarjejeniyar, wanda ya ce; ta zo daidai da irin kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba yi, na kara bunkasa fannin kiwon dabbobi na kasar, musamman gannin yadda gwamnatin ke da yakinin cewa; yin kiwon dabbobin na zamani, zai kara haBaka fannin a kasar nan.

Shi ma a nasa jawabin, a madadin hukumar Manajan Bunkasa Samar da Madarar Shanu na kasa da kasa, Jason Schrier, ya yi maraba da kulla wannan yarjejeniyar wadda kuma ya danganta ta a matsayin wani mataki na kara haBaka hadakar kasa da kasa, ta bunkasa fannin kiwon dabbobi.

Ya bayyana cewa, a karkashin wannan yarjejeniyar, hukumar za ta kawo kwararru, inda hakan zai kara taimaka wa masu kiwon dabbobi da ke jihar ta Gombe, har na dogon zango.

An dai kafa wannan hukumar ce a shekarar 1909, wadda kuma ta ke ci gaba da zama kan gaba a fannin yin kiwon dabbobi ta hanyar amfani da fasahar kimiyyar zamani.

Gombe
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 
Gombe
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Dakile Harin ISWAP Da Boko Haram A Borno

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.