ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar New Zealand Kan Kiwon Dabbobi

by Abubakar Abba and Sulaiman
5 months ago
gombe

Gwamnatin Jihar Gombe da hukumar bunkasa fannin kiwon dabbobi na zamani (LIC) da ke kasar New Zealand, sun rattaba hannun yarjejeniyar bunkasa fannin kiwon dabbobi na zamani tare da kuma kara karfafa jurewar kiwo na kowane irin yanayi da kuma kara samar da wata sabuwar damar haBaka tattalin arzikin da ke fannin na jihar.

Sun kulla wannan yarjejeniyar ce, biyo bayan wata ziyara ta kwana biyu da Gwaman Jihar Muhammadu Inuwa Yahaya, ya jagoranci wata tawaga zuwa hukumar, inda ziyarar ta bayar da damar kulla wannan yarjejeniya.

  • Amurka Ta Kwace Kadarorin ‘Yan Nijeriya 8 Masu Alaka Da Boko Haram
  • Kisan Ƙare Dangi: Sojojin Amurka Sun Fara Aikin Samar Da Tsaro A Nijeriya

Isma’ila Uba Misilli, Darakta Janar na yada labaran gwamnan ya bayyana hakan a cikin sanarwar da ya fitar, inda sanarwar ta ce; a karkashin wannan yarjejeniya, Bangarorin biyu za su kaddamar da gudanar shirin bincken hadaka a tsakaninsu, wacce za a sanya jami’ar Jihar Gombe, domin gudanar da binciken, musamman kan yadda za a fito da damar jinsin dabbobi tare da kuma gabatar da sabon tsarin samar da Madarar Shanu da namansu.

ADVERTISEMENT

Gwamna Yahaya, a jawabinsa a wajen rattaba hannun yarjejeniyar ya danganta hadakar a matsayin mai matukar muhimmanci da kuma girma, musamman domin a kara bunkasa kokarin da gwamnatin jihar ke ci gaba da yi na haBaka fannin kiwon dabbobi.

Ya bayyana cewa, wannan shirin ya yi daidai da irin kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da yi, na saita fannin kiwon dabbobi na kasar, ta hanyar amfani da ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi ta tarayya.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Shi kuwa a nasa jawabin, babban ministan ma’aikatar bunkasa kiwon dabbobi, Idi Mukhtar Maiha, ya yaba da wannan yarjejeniyar, wanda ya ce; ta zo daidai da irin kokarin da gwamnatin tarayya ke ci gaba yi, na kara bunkasa fannin kiwon dabbobi na kasar, musamman gannin yadda gwamnatin ke da yakinin cewa; yin kiwon dabbobin na zamani, zai kara haBaka fannin a kasar nan.

Shi ma a nasa jawabin, a madadin hukumar Manajan Bunkasa Samar da Madarar Shanu na kasa da kasa, Jason Schrier, ya yi maraba da kulla wannan yarjejeniyar wadda kuma ya danganta ta a matsayin wani mataki na kara haBaka hadakar kasa da kasa, ta bunkasa fannin kiwon dabbobi.

Ya bayyana cewa, a karkashin wannan yarjejeniyar, hukumar za ta kawo kwararru, inda hakan zai kara taimaka wa masu kiwon dabbobi da ke jihar ta Gombe, har na dogon zango.

An dai kafa wannan hukumar ce a shekarar 1909, wadda kuma ta ke ci gaba da zama kan gaba a fannin yin kiwon dabbobi ta hanyar amfani da fasahar kimiyyar zamani.

Gombe
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
Gombe
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • Sulaiman
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Next Post
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Dakile Harin ISWAP Da Boko Haram A Borno

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.