Ƙungiyar haɗakar jam’iyyun adawa ta ƙasa, (CUPP) ta goyi bayan kiran da Tsagin ’Yan Majalisar Wakilai na marasa rinjaye suka yi wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya mayar da hankali kan magance matsalolin tsaro da tattalin arzikin ƙasa ko kuma ya shirya yin murabus.
CUPP ta bayyana cewa wajibi ne gwamnatin tarayya ta ɗauki matakan gaggawa domin magance matsanancin rashin tsaro, wahalhalun tattalin arziki da kuma ƙalubalen rayuwa da ke addabar ’yan Nijeriya.
A cikin wata sanarwa da Mukaddashin Shugaban Ƙungiyar na Ƙasa, Peter Ameh, ya sanya wa hannu a ranar Alhamis, ƙungiyar ta ce ta yi daidai da matsayar Tsagin ’Yan Majalisar marasa rinjaye, tana mai jaddada cewa ya kamata a auna nasarar kowace gwamnati ne da irin tasirin da take yi wajen inganta rayuwar al’umma.
Sanarwar ta ce shugabannin da aka zaɓa ta hanyar zaɓe suna da alhakin samar da shugabanci nagari da walwalar jama’a, kuma ya kamata a tuhume su da alhakin abin da suka kasa cimmawa idan ba su cika alƙawuran da suka ɗauka ba.
CUPP ta kuma nuna damuwa kan ci gaba da tabarbarewar tsaro da matsin tattalin arziki a sassan ƙasar, tana mai kira ga gwamnati da ta ƙara ƙaimi wajen magance matsalolin da ke fuskantar ’yan ƙasa.














Discussion about this post