Mambobi da dama na jam’iyyar APC, ciki har da wasu shugabannin jam’iyyar a matakin mazabu, sun fice daga APC zuwa jam’iyyar PDP a ƙaramar hukumar Adavi ta jihar Kogi.
Masu sauya shekar sun kuma bayyana goyon bayansu ga burin Sanata Natasha Hadiza Akpoti-Uduaghan na neman wa’adi na biyu a matsayin mai wakiltar mazabar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawa.
Wadanda suka sauya shekar, waɗanda galibinsu sun fito ne daga mazabar Adavi ta Yamma, sun haɗa da wasu manyan jami’an APC kamar shugaban matasa na jam’iyyar, wanda ya sanar da ficewarsa tare da wasu mambobi da magoya baya.
An gudanar da taron karɓar sabbin mambobin ne a ranar Litinin, inda magoya bayan jam’iyya, shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki suka hallara domin tarbar su zuwa PDP.
Haka kuma, ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Adavi/Okehi, Abdulrahaman Badamasuiy, ya halarci taron.
Da take jawabi ga mahalarta taron, Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta bayyana sauya shekar a matsayin wata alama da ke nuna ƙara amincewar jama’a da manufar PDP ta shugabanci mai haɗa kai, ci gaba da kuma ingantaccen wakilci.
Ta yi maraba da sabbin mambobin tare da yaba musu bisa matakin da suka ɗauka na shiga jam’iyyar adawa.














Discussion about this post