Da jimla daya za a iya takaita salon jagorantar harkokin duniya na kasashen yamma, wato maganar da tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka, Antony Blinken, ya fada, wadda ta kasance kamar haka: “A tsarin kasa da kasa, idan ba ka zauna a gefen teburin cin abinci ba, to, za ka zama cikin takardar oda. “Idan an bari kasashen yamma sun ci gaba da jagorantar harkokin duniya, to, za a ga yadda suke rikida karin kasashe masu tasowa zuwa “abincin dake cikin takardar oda”. Kuma dimbin abubuwan da suka auku a shekarun baya sun shaida gaskiyar hakan. Misali, rikice-rikicen da kasashen yamma suka tayar da su a yankuna daban daban sun haddasa tsaiko ga tsarin samar da kayayyaki, lamarin da ya sanya kasashen Afirka fuskantar mummunar matsalar hauhawar farashin kayayyaki, inda aka yi hasashen cewa, matsakaicin adadin hauhawar farashin kayayyaki a nahiyar Afirka a shekarar 2026 zai kai kaso 10.4%.
Haka zalika, manyan hukumomin tantance yanayin da ake ciki a fannin hada-hadar kudi, da kasashen yamma ke jan ragamarsu, sun kambama hadarin da masu zuba jari ke iya fuskanta a nahiyar Afirka, ta yadda suka raunana karfin kasashen Afirka na janyo jari, da kara musu wuya ta fuskar neman samun lamuni.
Kusan duk wata manufar da kasashen yamma suka fitar, ta kan zama mai lahanta moriyar kasashe masu tasowa. Saboda haka, lokaci ya yi da za a jefa “teburin cin abinci” na kasashen yamma mai salon “kashin dankali” cikin kwandon shara.
To, hakan shi ne dalilin da ya sa kasar Sin ke ba da shawara ga kasashen duniya, don a gina wani tsarin jagorantar harkokin duniya mai nuna adalci da sanin-ya-kamata. A watan Satumban bara, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar inganta tsarin jagorantar harkokin duniya, wadda ta jaddada muhimmancin wasu ka’idoji 5, wato tabbatar da daidaiton ikon mulkin kai na kasashe daban daban, da kula da harkokin kasa da kasa bisa doka, da sanya bangarori daban daban cudanya da hadin kai tsakaninsu, da dora moriyar jama’a a kan sauran harkoki, da daukar takamaiman matakai masu amfani.
Sa’an nan a jiya, gwamnatin kasar Sin ta gabatar da takardar bayani mai alaka da aikin jagorantar harkokin duniya, wadda ta bayyana matakan da kasar Sin ta dauka a kokarin aiwatar da shawarar inganta tsarin jagorantar harkokin duniya.
Tunanin kasar Sin game da tsarin jagorantar harkokin duniya, wanda ya dora muhimmanci kan adalci maimakon karfi da iko, ya samu karbuwa daga dimbin kasashe masu tasowa. Kana bayan da kasar ta gabatar da shawarar jagorantar harkokin duniya, nan take ta samu goyon baya daga kimanin kasashe da kungiyoyin kasa da kasa 160, ciki har da tarayyar Najeriya.
Masana da ‘yan jarida da yawa daga kasashen Afirka ma sun amince da shawarar da kasar Sin ta bayar kan inganta tsarin jagorantar harkokin duniya. Inda shahararren dan jarida a Najeriya Lawal Sale, ya rubuta a cikin wani sharhinsa cewa, “Wannan shawara za ta haifar da karin kwanciyar hankali, da yanayi na tabbas a duniyarmu mai cike da tashin hankali, musamman ma a nahiyar Afirka.” Kana a nasa bangare, Paul Frimpong, wani shehun malami dan kasar Ghana, ya ce shawarar nan “tana tabbatar da cewa tsarin jagorancin duniya ba zai ci gaba da zama karkashin mallakar wasu kasashe masu karfi ba.” Kana dan jaridar kasar Lesotho, Silence Charumbira, ya ce shirin na baiwa kananan kasashe damar zama masu hakikanin ‘yancin kai.
A nasa bangare, Saxon Zvina, shahararren marubuci dan kasar Zimbabwe, ya bayyana cikin wata makalarsa cewa, ko da yake an gabatar da shawarar inganta tsarin jagorantar harkokin duniya bisa nagartacciyar niyyar gina tsarin duniya mai nuna adalci da sanin-ya-kamata, amma yunkurin cika wannan burin da aka sanya na fuskantar kalubale, ganin yadda bangarorin da suka amfana daga tsarin jagorancin duniya na yanzu za su ki yarda da gudanar da gyare-gyare, kana tsanantar takarar siyasa ita ma tana haifar da cikas ga yunkurin kawo sauye-sauye.
Ko za a iya daidaita tsarin jagorancin duniya cikin nasara, ko kuma akasin haka, ya danganta da niyyar gamayyar kasa da kasa ta daukar mataki cikin hadin gwiwa. Idan ba a son sake ganin wannan mummunan “teburi” na mai da kasashe marasa karfi a matsayin “abinci”, to, yanzu lokaci ya yi na yin kokari tare don jefa “teburin” cikin kwandon shara. (Bello Wang)















Discussion about this post