ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

by Sulaiman
3 weeks ago

Da jimla daya za a iya takaita salon jagorantar harkokin duniya na kasashen yamma, wato maganar da tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka, Antony Blinken, ya fada, wadda ta kasance kamar haka: “A tsarin kasa da kasa, idan ba ka zauna a gefen teburin cin abinci ba, to, za ka zama cikin takardar oda. “Idan an bari kasashen yamma sun ci gaba da jagorantar harkokin duniya, to, za a ga yadda suke rikida karin kasashe masu tasowa zuwa “abincin dake cikin takardar oda”. Kuma dimbin abubuwan da suka auku a shekarun baya sun shaida gaskiyar hakan. Misali, rikice-rikicen da kasashen yamma suka tayar da su a yankuna daban daban sun haddasa tsaiko ga tsarin samar da kayayyaki, lamarin da ya sanya kasashen Afirka fuskantar mummunar matsalar hauhawar farashin kayayyaki, inda aka yi hasashen cewa, matsakaicin adadin hauhawar farashin kayayyaki a nahiyar Afirka a shekarar 2026 zai kai kaso 10.4%.

Haka zalika, manyan hukumomin tantance yanayin da ake ciki a fannin hada-hadar kudi, da kasashen yamma ke jan ragamarsu, sun kambama hadarin da masu zuba jari ke iya fuskanta a nahiyar Afirka, ta yadda suka raunana karfin kasashen Afirka na janyo jari, da kara musu wuya ta fuskar neman samun lamuni.

Kusan duk wata manufar da kasashen yamma suka fitar, ta kan zama mai lahanta moriyar kasashe masu tasowa. Saboda haka, lokaci ya yi da za a jefa “teburin cin abinci” na kasashen yamma mai salon “kashin dankali” cikin kwandon shara.

ADVERTISEMENT

To, hakan shi ne dalilin da ya sa kasar Sin ke ba da shawara ga kasashen duniya, don a gina wani tsarin jagorantar harkokin duniya mai nuna adalci da sanin-ya-kamata. A watan Satumban bara, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar inganta tsarin jagorantar harkokin duniya, wadda ta jaddada muhimmancin wasu ka’idoji 5, wato tabbatar da daidaiton ikon mulkin kai na kasashe daban daban, da kula da harkokin kasa da kasa bisa doka, da sanya bangarori daban daban cudanya da hadin kai tsakaninsu, da dora moriyar jama’a a kan sauran harkoki, da daukar takamaiman matakai masu amfani.

Sa’an nan a jiya, gwamnatin kasar Sin ta gabatar da takardar bayani mai alaka da aikin jagorantar harkokin duniya, wadda ta bayyana matakan da kasar Sin ta dauka a kokarin aiwatar da shawarar inganta tsarin jagorantar harkokin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Tunanin kasar Sin game da tsarin jagorantar harkokin duniya, wanda ya dora muhimmanci kan adalci maimakon karfi da iko, ya samu karbuwa daga dimbin kasashe masu tasowa. Kana bayan da kasar ta gabatar da shawarar jagorantar harkokin duniya, nan take ta samu goyon baya daga kimanin kasashe da kungiyoyin kasa da kasa 160, ciki har da tarayyar Najeriya.

Masana da ‘yan jarida da yawa daga kasashen Afirka ma sun amince da shawarar da kasar Sin ta bayar kan inganta tsarin jagorantar harkokin duniya. Inda shahararren dan jarida a Najeriya Lawal Sale, ya rubuta a cikin wani sharhinsa cewa, “Wannan shawara za ta haifar da karin kwanciyar hankali, da yanayi na tabbas a duniyarmu mai cike da tashin hankali, musamman ma a nahiyar Afirka.” Kana a nasa bangare, Paul Frimpong, wani shehun malami dan kasar Ghana, ya ce shawarar nan “tana tabbatar da cewa tsarin jagorancin duniya ba zai ci gaba da zama karkashin mallakar wasu kasashe masu karfi ba.” Kana dan jaridar kasar Lesotho, Silence Charumbira, ya ce shirin na baiwa kananan kasashe damar zama masu hakikanin ‘yancin kai.

A nasa bangare, Saxon Zvina, shahararren marubuci dan kasar Zimbabwe, ya bayyana cikin wata makalarsa cewa, ko da yake an gabatar da shawarar inganta tsarin jagorantar harkokin duniya bisa nagartacciyar niyyar gina tsarin duniya mai nuna adalci da sanin-ya-kamata, amma yunkurin cika wannan burin da aka sanya na fuskantar kalubale, ganin yadda bangarorin da suka amfana daga tsarin jagorancin duniya na yanzu za su ki yarda da gudanar da gyare-gyare, kana tsanantar takarar siyasa ita ma tana haifar da cikas ga yunkurin kawo sauye-sauye.

Ko za a iya daidaita tsarin jagorancin duniya cikin nasara, ko kuma akasin haka, ya danganta da niyyar gamayyar kasa da kasa ta daukar mataki cikin hadin gwiwa. Idan ba a son sake ganin wannan mummunan “teburi” na mai da kasashe marasa karfi a matsayin “abinci”, to, yanzu lokaci ya yi na yin kokari tare don jefa “teburin” cikin kwandon shara. (Bello Wang)

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
  • Sulaiman
    Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

MASU ALAKA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Next Post
Tinubu

Rashin Tsaro: CUPP Ta Goyi Bayan Kiran Da Aka Yi Wa Tinubu Na Jagoranci Ko Murabus

LABARAI MASU NASABA

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.