Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mutane 16, da suka haɗa da maza 6 da mata 10, yayin wani samamen dare da ta kai a wasu wuraren da ake zargin ana aikata ayyukan da suka saɓa wa tarbiyya da ɗabi’a a cikin birnin Kano.
Mataimakin Kwamandan Hukumar Hisbah, Dr. Mujahideen Aminudeen, ya bayyana hakan ga manema labarai a ranar Alhamis, inda ya ce an gudanar da samamen ne a daren Laraba, 17 ga Yuni, 2026.
A cewarsa, jami’an Hisbah sun kai samamen ne a Kanem Suites da ke kan titin Yahaya Gusau, hanyar da ta nufi Jami’ar Bayero, da kuma yankin Danbare da Shisha Line a cikin birnin Kano.
Dr. Aminudeen ya ce matakin ya biyo bayan korafe-korafe da dama da hukumar ta samu daga al’umma, inda ake zargin ana aikata ayyukan rashin ɗa’a a wuraren.
Ya ce, “Mun samu korafe-korafe masu yawa game da waɗannan wurare kafin mu tura jami’anmu. A sakamakon samamen, mun kama mata goma da maza shida daga wurare daban-daban.”
Hukumar ta ce za ta ci gaba da gudanar da irin waɗannan ayyuka domin tabbatar da kiyaye ɗabi’u da bin dokokin addini da na jihar.














Discussion about this post