Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a Majalisar Dinkin Duniya, Sun Lei, ya gabatar da jawabi na gama-gari a taron kasashe masu rattaba hannu kan yarjejeniyar MDD game da dokokin teku karo na 36, inda ya bayyana matsayin kasar Sin game da yadda wasu kasashe suka sake tada hankali kan abin da ake kira wai “Hukuncin shari’ar tekun kudancin kasar Sin”.
A cikin jawabinsa a jiya, Sun Lei ya jaddada cewa, “Hukuncin shari’ar tekun kudancin kasar Sin” ya saba wa ka’idar “samun amincewa daga kasa”. “Kotun sulhun” ta yi shari’ar da ta fi karfin ikonta, ta karkatar da hukunci, don haka “hukuncin” da ta yanke ba bisa doka ba ne kuma ba shi da wani tasiri. “Hukunci shari’ar tekun kudancin kasar Sin” wata tsokana ce ta siyasa da ke sanye da rigar doka, da nufin musanta ikon mallakar yanki da hakkokin teku na kasar Sin a tekun kudancin kasar.
Tun da farko, kasar Sin ba ta amince da wannan “hukuncin” ba, kuma ba ta karbe shi ba. Wannan “hukuncin” ba zai taba shafar ikon mallakar yanki da hakkokin teku na kasar Sin a tekun kudancin kasar ba a ko a wane halin ake ciki. (Bilkisu Xin)















Discussion about this post