Ana gudanar da taro na 62 na majalisar kula da hakkin dan Adam ta Majalisar Dinkin Duniya a birnin Geneva na kasar Switzerland, inda mataimakiyar shugaban tawagar kasar Sin Li Xiaomei ta bayyana matsayin kasarta a gun taron da aka yi a ranar 16 ga watan nan.
Jami’ar ta bayyana cewa, harkokin hakkin dan Adam na duniya na fuskantar kalubale. Albarkacin cika shekaru 20 da kafa majalisar kare hakkin dan Adam ta MDD, ya dace a girmama hanyar raya hakkin dan Adam da kasa da kasa suka zaba, kuma ya kamata ofishin OHCHR ya taka muhimmiyar rawa.
Jami’ar ta kuma ce, kwanan nan kasar Sin ta bullo da shiri na biyar na daukar matakan kare hakkin dan Adam na duk kasa, a wani kokari na sanya tabbaci da zaman karko ga ci gaban sha’anin kare hakkokin dan Adam na duniya bisa ci gaban hakkokin dan Adam na kasar Sin.
Ta ce a halin yanzu, akwai zaman lafiya da jin dadin jama’a a jihohin Xinjiang da Xizang na kasar Sin, a yankin Hongkong ma jama’a na samun tabbacin halastattun hakkokinsu. Kazalika kuma, dokar ingiza hadin gwiwa da ci gaban al’ummomin Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin tana bada tabbaci ga bai wa al’ummomi hakkoki daidai-wa-daida, da sa kaimi ga ci gabansu cikin hadin gwiwa. (Murtala Zhang)















Discussion about this post