Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Joash Amupitan, ya gargadi cewa yawaitar matsalolin tsaro a sassa daban-daban na Nijeriya na barazana ga gudanar da sahihin zaɓe.
Ya bayyana hakan ne yayin wata ziyara da ya kai wa Sufeto Janar na ‘yansanda, Tunji Disu, a Abuja, a daidai lokacin da shirye-shiryen babban zaɓen 2027 ke ƙara ƙaratowa.
A cewarsa, matsalolin tsaro da suka haɗa da tashin hankali da barazanar kawo cikas ga harkokin zaɓe na iya lalata sahihancin zaɓe idan ba a ɗauki matakan da suka dace ba.
Amupitan ya jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da cewa an gudanar da zaɓe cikin lumana, gaskiya da adalci a fadin ƙasar.















Discussion about this post