A yau Laraba 6 ga Mayun 2026, mamban hukumar siyasa ta kwamitin tsakiya na JKS, kana ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya gana da ministan harkokin wajen kasar Iran, Sayed Abbas Aragchi, a birnin Beijing.
An ruwaito Aragchi yana bayyana halin da ake ciki game da tattaunawar Iran da Amurka da kuma abubuwa na gaba da Iran za ta yi la’akari da su, inda ya yi nuni da cewa, Iran za ta kiyaye ’yancin kanta da kiyaye martabar yankunanta, kana za ta nemi cikakkiyar mafita ta dindindin ta hanyar tattaunawar sulhu.
Ya kuma ce, Iran ta aminta da kasar Sin kuma tana sa ran Sin za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen karfafa zaman lafiya da kawo karshen yakin.
A nasa bangaren, Wang Yi ya bayyana cewa, Sin tana goyon bayan Iran wajen kare ’yancin kanta da kiyaye tsaronta. Sin ta yi amannar cewa, Iran tana da halastaccen ’yancin amfani da makamashin nukiliya na zaman lumana.
Kazalika, Sin tana yekuwar cewa, ya kamata kasashen yankin Gulf da na Gabas ta Tsakiya su karbi ragamar jagorantar makomarsu da kansu, tare da karfafa gwiwar Iran da karin kasashen Gulf su hau teburin tattaunawa da kuma cimma kyakkyawar alaka ta makwabtaka a tsakaninsu. (Mai Fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post