ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina Kasa

by Sulaiman
23 hours ago
Matasa

Ana wa matasa kirari daban-daban a cikin al’umma, tun daga lokacin yarinta da ake ce musu “yara manyan gobe” har zuwa cewa “matasa su ne kashin bayan ci gaban al’umma”, domin nuna irin muhimmancin da suke da shi ga raya ci gaban kasa da kuma al’umma baki daya.A kasar Sin, tun yara suna kanana ake renonsu game da kishin gina kasa.

Ana sanar da su muhimman abubuwa da suka shafi aiki tukuru, da tambarin kasa kamar tuta da taurarin cikinta da ma’anarsu, da muhimman wurare masu nasaba da gina ci gaban kasar ta fuskar tattalin arziki da zamantakewa har kuma zuwa lokacin da za su kai shekarun balaga da za su fara shiga cikin harkokin raya kasa ka’in-da-na’in.Irin wannan tarbiyya mai ban sha’awa, ana koyar da ita ta hanyoyi da dama, tun daga cikin iyali, zuwa makarantu da kuma kafofin watsa labarai.

Akwai wani shiri na gidan rediyo da aka fara gabatar da shi tun a ranar 4 ga Satumbar 1956 mai suna Xiaolaba, wato “karamin kakaki” da ya kasance shirin rediyo na farko a Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin da aka kebe musamman domin yaran da ba su kai shekarun shiga makaranta ba.

ADVERTISEMENT

Shirin wanda ya gawurta har ya zama babban shirin da ake watsawa a rediyo, da talabijin, da shafukan sada zumunta da shirye-shiryen yada labarai na cikin makarantu, yana bayar da labarai ne masu dadi ga yara dake kunshe da hikimomi da sauran al’amura da suka shafi gina tunanin yara a turba mai kyau.

A lokacin da shugaban kasar Sin Xi Jinping yake taya murnar cika shekaru 70 da fara gabatar da wannan shiri, ya jaddada kira ga kwararru a fannin tarbiyyantar da yara su kara azama wajen renon matasa su zamo masu kwarewa don su ci gaba da raya tafarkin gurguzu.

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Kazalika, a wani jawabi da na ci karo da shi kwanan nan na shugaba Xi, na ga yadda ya ba da muhimmanci sosai a kan kira ga matasa su rika daidaita burikansu na rayuwa da na ci gaban kasa, inda hakan ke nuna muhimmancin gudunmawar matasan ga raya kasa. Kazalika, a wani bangare na kokarin da ake yi a kan renon matasa a turbar gina ci gaban kasa da hidimta wa al’umma, jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin kan tura matasa da suka yi rajistar zama mambobinta zuwa yankunan karkara domin gudanar da ayyukan hidimta wa jama’a ko da kuwa daga birane suka fito. Haka nan, ana tura kwararrun matasa daga fannonin ilimin aikin gona zuwa kauyuka don taimaka wa manoma da dabarun aiki na zamani.

Tabbas, irin wannan reno da kasar Sin ke wa matasa a kan kyakkyawar turba, ya sa matasan kasar nuna jajircewa wajen ba da gudunmawa ga ci gaban kasar ta fuskoki da dama, walau a karkashin kungiyoyinsu ko dandalolinsu.

Kuma ya dace musamman ga kasashe masu tasowa, su ba da karfi ga renon matasansu a kyakkyawar turba domin taimaka wa burikansu na gina kakkarfan ci gaban kasa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Matasa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
  • Sulaiman
    Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
  • Sulaiman
    Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

MASU ALAKA

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
Daga Birnin Sin

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Next Post
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 - Remi Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Matasa

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Matasa

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.