ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

RIGATA 2026: Jama’a Daga Ciki Da Wajen Nijeriya Za Su Baje Kolin Al’adun Gargajiya 

by Sulaiman
5 months ago

Daga Bello Hamza

Alummar Masarautar Yauri da ke a kudancin Jihar Kebbi, sun shirya tsaf, domin gudanar da bikin gargajiya na Rigata da ake sa ran zai gudana a cikin farkon shekera mai kamawa.

 

ADVERTISEMENT

An shafe sama da shekaru 200 ana gudanar da wannan bikin gargajiyar wanda kuma ba a ciki ganin irinsa, a kasar nan ba, saboda ana gudanar da bikin ne, kan tudu da kuma gudanar da wasanni, a kan Kogin Neja.

  • Sin Ta Nuna Adawa Da Kalaman Jami’in Japan Game Da Mallakar Makaman Nukiliya
  • AFCON 2025: Ƙasashe 5 Da Za Su Iya Lashe Gasar Nahiyar Afirka

Bikin na da nasaba da hudda a tsakanin ‘yan Adam da kuma dabbibin ruwa, kamar Dorinar ruwa, Kada wadanda suke ke kai wa bil Adama hari, tare da janyo mutuwar su.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

 

Domin a dakile wannan barazanar hakan ke sanya wa a duk shekara, jaruman Gungu, suke shiga cikin Kwale-Kwale dauke da makamai suna farautar irin wadannan mugayen dabbobin ruwan.

 

Suna kuma yin hakan ne, domin su samar da tsaro a kan Kogunna da tabbatar da zirga-zirga a cikin sauki da kuma kara habaka sauran hada-hadar kawuanci a Kogunan.

 

Bayan zuwa Turwan mallaka a karni na 19, an haramta farautar Dorinar ruwa, sai dai, daga baya, an ci gaba da yi a bikin na Rigata, domin a nuna irin karfin da Masarautar take da shi, musamman a lokutan bukukuwan aure.

 

Kai ziyarar da marigayi Sardaunan Sokoto kuma Firimiyan Arewa Sir Ahmadu Bello, a yankin na Yauri, hakan ya sake farfado da bikin na Rigata, wanda lokacin ziyararsa, aka gudanar da wasanni da kuma baje kolin amfanin gona, domin a karrama shi.

 

Bisa jajircewar Mai Martaba Sarkin Yauri Dakta Mohammad Zayyanu Abdullahi, CON, da kuma namjin kokarin gwamnan jihar, an sake farfado da bikin karo na 45.

 

Mayar da hankali da Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris kuma, Kauran Gwandu, Gamjin Yauri, ya taimaka matuka wajen farfado da martabar bikin.

 

Kazalila, tsarin da Gwamna Idris ya samar na daga darajar yawon bude Ido a jihar, hakan ya kara janyo ra’ayin bunkasar bukukuwan gargajiya a jihar.

 

Misali, manya bukukuwan gargajiya kamarsu, bikin kamun Kifi na kasa da kasa na Argungu da ake gudanarwa a garin Argungu,bikin gargajiya na the Uhola.

 

Bikin gargajiya na Zuru da ake yi a yankin Geandu, ya taimaka wajen daga darajar yawon bude Ido na Jihar Kebbi a Idon duniya.

 

Duba da yadda ake gudanar da manyan bukukuwan gargajiya a kasar, sai dai, akwai wasu manyan kalubale nan a ci gaba da gudanar da bukuwan da kuma karancin kudi, musamman domin a ci gaba da gudanar da bukukuwan.

 

Bukukuwa da dama, sun bace bat, saboda rashin kudin ci gaba da gudanar da su, wasu ma, tun daga matakin farkon fara gudanar da su.

 

Idan har ana son gudanar da bukukuwan gargajiya su ci gaba da dorewa, dole ne, alumma su bayar da na su goyon bayan, musamman wajen samar da kudade.

 

Bikin na Rigata, na daga cikin manyan bukuwan da ke a kasar ana kuma gudanar da bikin ne, a duk shekara a cikin watan Fabirairun.

 

Ana fara gudanar da bikin ne, ta hanyar baje kolin amfanin gona, sai kuma nuna al’adun gargajiya da kade-kade da kuma raye-raye, tare da yin gasar kokawar gargajiya.

 

A bikin ana gudanar da gasar wasa da Kwale-Kwale a kan Kogi, inda kuma a bikin ya hada da, ‘yan tawagar kai Amarya tare da yi mata rakiya da kade-kade a cikin Jirgin Kwale-Kwalen da aka yi masa ado

 

A shekarun baya, ana yi wa Amaryar rakia ne, zuwa gidan mijinsu a cikin Kwale-Kwale, musamman a yankunan da ake da Rafuka.

 

A yayin da ake shirye-shiryen gudanar da bkin na bana, ‘yan Nijeriya na ci gaba da sa ido, domin su ga yadda bikin na zai gabatar da wasu sabbin dabaru, musamman a bangaren kade-kade.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Babban Yankin Guangdong-Hong Kong-Macao Ya Zage Damtse Don Gina Babban Muhallin Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha Na Duniya

Babban Yankin Guangdong-Hong Kong-Macao Ya Zage Damtse Don Gina Babban Muhallin Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha Na Duniya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.