ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

by Rabi'u Ali Indabawa
5 hours ago
talauci

Wani sabon rahoto ya bayyana cewa matsalar rashin tsaro a Arewacin Nijeriya ba wai kawai yana ƙara tsananta talauci ba ne, har ma da raunana ƙarfin iyalai wajen farfaɗowa daga matsin tattalin arziki.

Rahoton mai taken “Rashin Tsaro, Hanyoyin Samun Abinci da Walwalar Jama’a a Arewacin Nijeriya” ya nuna cewa rikice-rikicen da ake fama da su a yankin na jefa mutane cikin talauci ta hanyoyi daban-daban, ciki har da rasa hanyoyin samun kuɗin shiga, lalacewar dukiyoyi, durkushewar kasuwanni da kuma ƙara jefa iyalai cikin mawuyacin hali.

An gabatar da sakamakon rahoton ne a wani taron Intanet da Chronic Poɓerty Adɓisory Network (CPAN) na Cibiyar Nazarin Ci Gaba ta Birtaniya, tare da Cibiyar Bincike da Ayyukan Ci Gaba da kuma shirin Ƙarfafa Zaman Lafiya da Juriya a Nijeriya (SPRiNG) mai samun tallafi daga Ma’aikatar Harkokin Waje, Ƙungiyar Commonwealth da Ci Gaba ta Birtaniya (FCDO) suka shirya.

ADVERTISEMENT

Da take gabatar da rahoton, mataimakiyar daraktar CPAN, Dakta Ɓidya Diwakar, ta ce binciken ya gano manyan nau’o’i uku na matsalolin tsaro da ke addabar Arewacin Nijeriya. Waɗannan sun haɗa da hare-haren Boko Haram/ISWAP a Arewa maso Gabas, rikicin manoma da makiyaya a Arewa ta Tsakiya, da kuma ayyukan ƴan bindiga da masu garkuwa da mutane a Arewa maso Yamma.

A cewarta, hare-haren Boko Haram da ISWAP sun fi yin mummunan tasiri ga rayuwar iyalai, inda gidajen da abin ya shafa suka samu raguwar kashe kuɗaɗen rayuwa da kaso tsakanin 8 zuwa 14 cikin 100 idan aka kwatanta da sauran gidaje a cikin shekaru biyu kafin gudanar da binciken. Haka kuma, bashin da rikice-rikicen suka haifar tun daga sheƙarar 2009 ya ƙara janyo asarar kashi 8 zuwa 13 cikin 100 ga waɗannan iyalai.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

Rahoton ya kuma nuna cewa rikicin manoma da makiyaya ya fi shafar iyalan da ke dab da faɗawa cikin talauci a yankin Arewa ta Tsakiya, inda ya haddasa raguwar kashe kuɗaɗen rayuwa da kashi 14 cikin 100 ga iyalan da ke matakin kashi na 60 cikin 100 na samun kuɗin shiga. Haka kuma, ayyukan ƴan bindiga da masu garkuwa da mutane a Arewa maso Yamma sun jawo raguwar kashe kuɗaɗen rayuwa da tsakanin kashi 4 zuwa 11 cikin 100, musamman ga iyalan da ke cikin matsakaicin talauci.

Duk da wannan mummunan yanayi, rahoton ya bayyana cewa faɗaɗa hanyoyin samun kuɗin shiga su ne hanyoyi mafiya inganci na fita daga talauci.

Rahoton ya ce, “Haɗa hanyoyin samun kuɗin shiga daga noma, ayyukan da ba na noma ba da kuma ƙananan sana’o’i su ne matakan kariya mafi tasiri ga iyalai a dukkan nau’o’in rikice-rikicen da aka yi nazari a kansu.”

Sai dai binciken ya nuna cewa kashi 13 cikin 100 kacal na shugabannin gidaje a Arewacin Nijeriya ne ke da hanyoyin samun kuɗin shiga fiye da guda ɗaya.

Har ila yau, rahoton ya nuna cewa ilimi na ƙara wa iyalai damar faɗaɗa hanyoyin samun kuɗin shiga, amma gidajen da mata ko matasa ke jagoranta, waɗanda suka kai kashi 28.9 cikin 100 na gidaje a yankin, ba sa cin gajiyar irin waɗannan damammaki yadda ya kamata.

Da yake jawabi a taron, Ministan Harkokin Jin Ƙai da Rage Talauci, Bernard Doro, ya yi alƙawarin ci gaba da haɗa gwiwa da masu ruwa da tsaki, tare da buƙatar masu bincike su samar da ƙarin hujjoji da bayanai kan hanyoyin tantance waɗanda suka cancanta, tsara yadda za a aiwatar da shirye-shirye, da kuma hanyoyin da za su taimaka wa jama’a su fita daga talauci a ƙarƙashin shirin gwamnati na ” Tsarin Ba da Agajin Jin Ƙai da Martani Ɗaya Don Yaƙi da Talauci. “musamman domin tallafa wa mata da matasa da galibi ake bari a baya.

talauci
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Noma
Rahotonni

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Next Post
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Kotu Ta Soke Rajistar Jam'iyyar NDC A Matsayin Jam'iyyar Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
sikila

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 26, 2026
makarfi

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026
Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.