ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
talauci

Wani sabon rahoto ya bayyana cewa matsalar rashin tsaro a Arewacin Nijeriya ba wai kawai yana ƙara tsananta talauci ba ne, har ma da raunana ƙarfin iyalai wajen farfaɗowa daga matsin tattalin arziki.

Rahoton mai taken “Rashin Tsaro, Hanyoyin Samun Abinci da Walwalar Jama’a a Arewacin Nijeriya” ya nuna cewa rikice-rikicen da ake fama da su a yankin na jefa mutane cikin talauci ta hanyoyi daban-daban, ciki har da rasa hanyoyin samun kuɗin shiga, lalacewar dukiyoyi, durkushewar kasuwanni da kuma ƙara jefa iyalai cikin mawuyacin hali.

An gabatar da sakamakon rahoton ne a wani taron Intanet da Chronic Poɓerty Adɓisory Network (CPAN) na Cibiyar Nazarin Ci Gaba ta Birtaniya, tare da Cibiyar Bincike da Ayyukan Ci Gaba da kuma shirin Ƙarfafa Zaman Lafiya da Juriya a Nijeriya (SPRiNG) mai samun tallafi daga Ma’aikatar Harkokin Waje, Ƙungiyar Commonwealth da Ci Gaba ta Birtaniya (FCDO) suka shirya.

ADVERTISEMENT

Da take gabatar da rahoton, mataimakiyar daraktar CPAN, Dakta Ɓidya Diwakar, ta ce binciken ya gano manyan nau’o’i uku na matsalolin tsaro da ke addabar Arewacin Nijeriya. Waɗannan sun haɗa da hare-haren Boko Haram/ISWAP a Arewa maso Gabas, rikicin manoma da makiyaya a Arewa ta Tsakiya, da kuma ayyukan ƴan bindiga da masu garkuwa da mutane a Arewa maso Yamma.

A cewarta, hare-haren Boko Haram da ISWAP sun fi yin mummunan tasiri ga rayuwar iyalai, inda gidajen da abin ya shafa suka samu raguwar kashe kuɗaɗen rayuwa da kaso tsakanin 8 zuwa 14 cikin 100 idan aka kwatanta da sauran gidaje a cikin shekaru biyu kafin gudanar da binciken. Haka kuma, bashin da rikice-rikicen suka haifar tun daga sheƙarar 2009 ya ƙara janyo asarar kashi 8 zuwa 13 cikin 100 ga waɗannan iyalai.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Rahoton ya kuma nuna cewa rikicin manoma da makiyaya ya fi shafar iyalan da ke dab da faɗawa cikin talauci a yankin Arewa ta Tsakiya, inda ya haddasa raguwar kashe kuɗaɗen rayuwa da kashi 14 cikin 100 ga iyalan da ke matakin kashi na 60 cikin 100 na samun kuɗin shiga. Haka kuma, ayyukan ƴan bindiga da masu garkuwa da mutane a Arewa maso Yamma sun jawo raguwar kashe kuɗaɗen rayuwa da tsakanin kashi 4 zuwa 11 cikin 100, musamman ga iyalan da ke cikin matsakaicin talauci.

Duk da wannan mummunan yanayi, rahoton ya bayyana cewa faɗaɗa hanyoyin samun kuɗin shiga su ne hanyoyi mafiya inganci na fita daga talauci.

Rahoton ya ce, “Haɗa hanyoyin samun kuɗin shiga daga noma, ayyukan da ba na noma ba da kuma ƙananan sana’o’i su ne matakan kariya mafi tasiri ga iyalai a dukkan nau’o’in rikice-rikicen da aka yi nazari a kansu.”

Sai dai binciken ya nuna cewa kashi 13 cikin 100 kacal na shugabannin gidaje a Arewacin Nijeriya ne ke da hanyoyin samun kuɗin shiga fiye da guda ɗaya.

Har ila yau, rahoton ya nuna cewa ilimi na ƙara wa iyalai damar faɗaɗa hanyoyin samun kuɗin shiga, amma gidajen da mata ko matasa ke jagoranta, waɗanda suka kai kashi 28.9 cikin 100 na gidaje a yankin, ba sa cin gajiyar irin waɗannan damammaki yadda ya kamata.

Da yake jawabi a taron, Ministan Harkokin Jin Ƙai da Rage Talauci, Bernard Doro, ya yi alƙawarin ci gaba da haɗa gwiwa da masu ruwa da tsaki, tare da buƙatar masu bincike su samar da ƙarin hujjoji da bayanai kan hanyoyin tantance waɗanda suka cancanta, tsara yadda za a aiwatar da shirye-shirye, da kuma hanyoyin da za su taimaka wa jama’a su fita daga talauci a ƙarƙashin shirin gwamnati na ” Tsarin Ba da Agajin Jin Ƙai da Martani Ɗaya Don Yaƙi da Talauci. “musamman domin tallafa wa mata da matasa da galibi ake bari a baya.

talauci
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Kotu Ta Soke Rajistar Jam'iyyar NDC A Matsayin Jam'iyyar Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.