ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2025: Ƙasashe 5 Da Za Su Iya Lashe Gasar Nahiyar Afirka

by Sadiq Usman
6 months ago

A ranar Lahadi aka fara gasar Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) ta 2025 a Birnin Rabat, da ke Ƙasar Morocco, inda mai masaukin baƙi ta doke Comoros da ci 2–0, wanda hakan ya sa ta fara gasar da ƙafar dama. 

Brahim Díaz da Ayoub El Kaabi ne suka zura ƙwallayen biyu bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, lamarin da ya nuna irin ƙwarewa da ƙarfi da tawagar ke da shi, wanda ya sa ake kallon su a matsayin waɗanda za su iya lashe gasar.

  • Xi Ya Taya Jose Antonio Kast Murnar Lashe Zaben Shugaban Chile

Ƙasashe 24 ne suka samu gurbin zuwa gasar ta bana, inda ake sa ran za a buga wasanni masu zafi cike da armashi.

ADVERTISEMENT

Daga cikin ƙasashen da za su fafata akwai manyan ƙasashe irin su Morocco, Masar, Senegal, Aljeriya, Nijeriya, Côte d’Ivoire, Kamaru, Afirka ta Kudu, DR Congo, Mali, Tunisiya, da sauran ƙasashe kamar Comoros, Sudan, Angola, Zambia, Uganda, da Benin.

Manyan Ƙasashen Da Ake Hasashen Za Su Iya Lashe Gasar Ta Bana

1. Moroko — A matsayinta na mai masaukin baƙi na gasar, kuma ɗaya daga cikin ƙasashen Afirka mafi ƙarfi a duniya, Morocco ta fara gasar AFCON ta 2025 a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen da ake shakka. Samun gogaggen mai horaswa, samun goyon bayan magoya baya a gida, da kuma haziƙan ’yan wasa, ya sa sun zama sahun gaba wajen neman lashe gasar. Tawagar tana fatan kawo ƙarshen dogon lokaci da ta shafe ba tare da lashe gasar ba.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

2. Masar — Masar, wadda ta lashe AFCON sau bakwai a tarihin gasar, ta shiga gasar da tarihi da kuma dogaro da fitaccen ɗan wasan nan, Mohamed Salah, wanda ke da burin jagorantar Pharaohs zuwa nasara.

Tarihi da ƙwarewarsu a wannan gasa ya sa suka zama barazana ga kowace ƙasa.

3. Senegal — Zakunan Teranga, zakarun AFCON na 2021, har yanzu suna daga cikin manyan ƙasashen Afirka. Suna da tawagar ƙwararrun ‘yan wasa, suna buga ƙwallo cikim sauri da tsari mai kyau, wanda hakan ya sa abokan hamayya ke shakkarsu.

4.  Aljeriya — Ana musu kirari da masu abun ban mamaki. Ko da yake Aljeriya ta fuskanci ƙalubale a ’yan shekarun baya, amma duk da haka har yanzu tana da ’yan wasa masu fasaha da gogewa.

5. Nijerya  — A gefe guda kuma, Nijeriya na da Super Eagles, wadda ke da ‘yan wasa masu cike da basira da ƙarfi a gaba. Nijeriya ta zama barazana a Afrika a baya-bayan nan duna da irin jajirtattun ‘yan wasan da ta haɗa da kuma gogaggen mai horaswa.

Sauran Ƙasashen da Za Su Iya Ba Da Mamaki

Ƙasashe irin su Côte d’Ivoire (zakarun gasar bara), Kamaru, Tunisiya, Afirka ta Kudu, Mali, da DR Congo su ma na da ƙwarewa da haziƙan ’yan wasa da za su iya taka wa manyan ƙasashe burki idan suka yi amfani da damar da suka samu.

Gasar AFCON ta 2025 na shirin zama ɗaya daga cikin gasar da za ta fi ɗaukar hankali duba da irin tanadi da shirin da masu masaukin baƙi suka yi.

Gasar ta haɗa manyan ƙasashen da suka shahara a tarihin ƙwallon ƙafar Afirka da kuma ƙasashe masu tasowa da ke shirin nuna bajintarsu. Duk da cewa Morocco na da fifiko saboda kasancewarsu masu masauki baƙi da kyakkyawan tsari, ƙasashe irin su Masar, Senegal, Nijeriya, da Côte d’Ivoire sun yi shiri na musamman domin fafatawa wajen lashe kofin na bana.

Masoya ƙwallon ƙafa a faɗin Afirka na sa ran ganin gasa mai cike da tsari, tarihi da abubuwan tunawa.

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Sin Ta Nuna Adawa Da Kalaman Jami’in Japan Game Da Mallakar Makaman Nukiliya

Sin Ta Nuna Adawa Da Kalaman Jami'in Japan Game Da Mallakar Makaman Nukiliya

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.