ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Kabilanci: An Fara Binciken Wasu Manyan Sarakuna A Kogi

by Sadiq
4 years ago
Sarakuna

Gwamnatin Jihar Kogi ta fara gudanar da bincike a kan wasu manyan sarakunan Jihar guda biyu game da wani mummunan tashin hankalin da ya yi sanadin mutuwar akalla mutane tara tare da kone gidaje da dama  a karamar hukumar Bassa da ke jihar.

Rahotanni dai sun nuna cewa manyan sarakunan guda biyu, masu daraja ta daya sun hada da Alh. Khalid Ali Bukar Sarkin Mozum, Sarkin Bassa da kuma Chif William Keke dukansu a yanzu haka suna hannun hukumomi a jihar domin gudanar da bincike a kan lamarin.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace DPO A Kaduna
  • G7 Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Taimakon Ukraine A Yakinta Da Rasha

Gwamnatin jihar dai ta ce yankin na Bassa ya dade yana fama da tashin hankali da ya shafi kabilanci da kuma rikicin mallakar filaye a tsakanin ‘yan kabilar Egbira da kuma Bassa Komo.

ADVERTISEMENT

Al’amarin da gwamnatin jihar ke gani sarakunan na da rawar takawa wajen shawo kan wannan matsala kamar yadda kwamishinan labarai na jihar Kogin Mr. Kinsley Fanwo, ya yi karin bayani, inda ya ce ba wai an kama su bane, an gayyace su ne domin su yi karin haske a kan matsaloli da dama da za su taimaka wajen dorewar zaman lafiya a wannan karamar hukuma ta Bassa.

Fanwo, ya ce gwamnati ta yi kokarin dawo da zaman lafiya a yankin, kuma akwai wani tsari da aka samar da zai hana aukuwar abin da ya faru a baya.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Daya daga cikin sarakunan yankin da aka kone gidansa sakamakon tashin hankalin, yanzu haka ya ke gudun hijira, wato Hakimin Mozum, Alh. Haruna Abubakar, ya ce duk da suna gudun hijira, a yanzu haka suna kokarin karbar Belin Babban sarkin nasu.

Masu sharhi a kan lamurran tsaro dai na ganin matakin rike manyan sarakunan yankin, watakila ya taimaka wajen gano bakin zaren da zai taimaka wajen shawo kan matsalar tashin-tashina da a aka dade ana fama da ita a yankin.

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
An Kashe Kasurgumin Dan Fashin Dajin Da Ya Addabi Mutane A Leren Jihar Kaduna

An Kashe Kasurgumin Dan Fashin Dajin Da Ya Addabi Mutane A Leren Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.