Mai neman takarar shugaban ƙasa a 2027, Peter Obi, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar ADC, yana mai danganta matakin da rikice-rikicen cikin gida da kuma matsalolin da tsarin siyasar Nijeriya ke fuskanta.
A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Lahadi, Obi ya bayyana matuƙar takaicinsa kan abin da ya kira “gurbatacciyar” yanayin siyasa mai cike da tsoratarwa, rashin tsaro da kuma rikice-rikicen cikin gida da ba sa ƙarewa.
“Mutane da yawa ba sa fahimtar irin raɗaɗin da wasu daga cikinmu ke ɗauka a kullum cikin shiru, wahalhalun da muke fuskanta a ɓoye, nauyin damuwa da kuma gwagwarmayar da muke yi yayin ƙoƙarin rayuwa da yi wa al’umma hidima cikin gaskiya a mawuyacin hali,” kamar yadda ya rubuta.
Tsohon gwamnan Jihar Anambra ya ce matakin da ya ɗauka na ficewa daga jam’iyyar haɗakar ‘yan adawa bai samo asali daga wata matsala ta ƙashin kai da shugabannin jam’iyyar ba.
Ya kuma wanke wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar daga duk wani zargi na laifi ko rashin gaskiya.















Discussion about this post