A baya-bayan nan, shugaban kasar Myanmar Min Aung Hlaing, ya yi fashin baki dangane da salo, da turbar zamanantawa irin ta Sin, inda ya ce, tun farkon sabon karbin nan, kasar Sin ta cimma manyan nasarori da suka ciri tuta. Ya ce, Sin ta samu ci gaba cikin sauri, har ma ya sha karanta labarai masu nasaba da bunkasar kasar a fannin kirkire-kirkiren fasahohi.
Kazalika, al’ummun kasar na zamanin yau, sun himmatu wajen samar da karin nasarori, sun kuma zamo karfin dake ingiza bunkasar kasar.Shugaban na Myanmar, wanda ya yi tsokacin yayin zantawa da kafar CMG ta kasar Sin, ya kara da cewa, ci gaban kasar Sin na gudana bisa daidaito.
Alal misali, biranen Beijing, da Shanghai, da Chongqing, da Guangzhou, na da kamanceceniya ta fuskar mizanin ci gaba da ‘yan bambance-bambance kadan. Don haka ci gaban kasar ta Sin ya zamo kyakkyawan misali ga kasar Myanmar.
Game da kwarewar Sin mafi burgewa ga Myanmar ta fuskar ciyar da kasa gaba kuwa, shugaba Min Aung Hlaing ya ce, Sin ta zamo wani dandalin koyi mai nagarta.
Ya ce sashen gine-gine ababen more rayuwa, fanni ne da sassan biyu za su iya yin hadin gwiwa a cikinsa. Kari kan hakan, Sin na da ci gaba ta fuskar fasahohin injiniya, da na laturoni, da kimiyya da fasaha, da fasahohin binciken samaniya, da kyankasa, da sarrafa hajojin masana’antu da dai sauransu, wadanda duka ke iya samar da dama ta hadin gwiwa. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post