ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
1 hour ago
Super Eagles

Duk da cewa tawagar Super Eagles ta Nijeriya ba ta samu tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta 2026 da aka fara daga ranar 11 ga watan Yuni ba a Amurka da Canada da kuma Meɗico.

Amma za a iya cewa ba a bar Nijeriya a baya ba wajen samun wakilai a gasar ta duniya. Bisa ƙididdiga, ƴan wasa 16 ƴan asalin Nijeriya ne za su wakilci ƙasashe dabandaban a tsakanin ƙasashe 48 a karon farko a tarihin gasar.

Kenan za a iya cewa rasa samun damar shiga gasar da Nijeriya ta yi ta bana, bai hana ta samun ƴan ƙwallonta da za su wakilce ta a babbar gasar ta duniya ba.

ADVERTISEMENT

Nijeriya tana da wakilci na daban a gasar wanda ba a kan sunan ƙasa kai tsaye bane amma ta hanyar ƴan ƙwallo fiye da 16 masu asalin Nijeriya da za su wakilci ƙasashe tara dabandaban a gasar da ake yi a yanzu. Wannan yana nuna yadda ƴan wasan Nijeriya suka bazu a faɗin duniya, suna taka rawa a manyan liglig na Turai da Amurka, har ma sun kai matakin wakiltar ƙasashen da suka taso ko suka girma a cikinsu.

Ga Sunayen ƴan Nijeriya guda 16 da suke wakiltar wasu ƙasashen a gasar kofin duniya

LABARAI MASU NASABA

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Ingila: Babbar cibiyar ƴan Nijeriya a gasar kofin duniya. Ingila ce ƙasar da ke da mafi yawan ƴan Nijeriya a wannan jerin. A nan za a ga wasu manyan taurari da suka yi fice a gasar Premier League: Bukayo Saka (Arsenal) An haifi ɗan wasa Bukayo Saka a Ingila, amma iyayensa ƴan Nijeriya ne daga ƙabilar Yarabawa.

Eberechi Eze (Arsenal) An haifi ɗan wasan a Ingila, amma iyayensa ƴan Nijeriya ne kuma yana ɗaya daga cikin ƴanwasan da kociyan tawagar Ingila, Thomas Tuchel ya gayyata domin buga gasar cin kofin na duniya.

Noni Madueke (Arsenal) Tsohon ɗan wasan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Chelsea ne kuma kamar Saka da Eze, an haife shi a Ingila, amma iyayensa daga Nijeriya suke daga ƙabilar Igbo.

Waɗannan ƴan wasa sun riga sun zama ginshiƙai a cikin tawagar Ingila da Arsenal, kuma suna daga cikin manyan sunaye da ake dogaro da su a gasar a daidai wannan lokaci.

Faransa:

Michael Olise (Bayern Munich), An haifi Olise a Ingila, kuma mahaifinsa ɗan Nijeriya ne da kuma mahaifiyarsa daga Aljeriya  ya samu damar wakiltar ƙasa uku da ya haɗa da Ingila da Nijeriya da kuma Faransa, hakan ya sa ya zabi buga wa tawagar Faransa wasa.

Ɗan wasan ya buga wasa tun farko a tawagar matasan Faransa da wakiltarta a gasar gujeguje da tsalletsalle ta Olympic, yanzu yana cikin babbar tawagar ƙasar a gasar cin kofin duniya. Tuni kuma Olise ya zama ɗaya daga cikin sabbin taurari da ke bai wa Faransa ƙarin ƙarfi a gurbin kai harehare a tawagar.

Jamus:

Jamal Musiala (Bayern Munich). An haifi ɗan wasan a birnin Stuttgart a Jamus, yana da fasfo biyu da yake riƙe da shi na Jamus da na Ingila. Tushen kuwa mahaifiyarsa ƴar Jamus ce da kuma mahaifinsa ɗan Nijeriya da kuma Ingila. Ya fara buga wa matasan Ingila wasa kafin daga baya ya zabi Jamus.

Musiala musamman ya zama ɗaya daga cikin fitattun ƴan wasa a Bundesliga, kuma yana daga cikin matasan da ake ganin za su iya canza wasa a kowane lokaci.

Feliɗ Nmecha (Borussia Dortmund). An haifi Feliɗ a birnin Hamburg a Jamus, kuma mahaifiyarsa daga Jamus take da mahaifinsa ɗan Nijeriya yana kuma da tsatson Ingila, ya kuma samu damar wakiltar Jamus ko kuma Ingila, wanda ya fara buga wasa a matasan Ingila daga baya ya sauya ya koma buga wasa a Jamus.

Austria: Dabid Alaba (Real Madrid). Yanzu ya bar Real Madrid, bayan da kwantiraginsa ya ƙare a ƙarshen kakar da aka kammala ta bana. Alaba yana wakiltar Austria, wanda aka haifa a birnin Ɓienna, shi ne ma kyaftin ɗin tawagar ƙasar. Mahaifinsa ɗan Nijeriya ne da kuma mahaifiyarsa daga Philippines.

Alaba ya shahara musamman a matsayin ɗaya daga cikin mafi kyawun masu tsaron baya a duniya, sai dai kuma ya yi fama da jinya, wataƙila wannan ce gasar kofin duniya ta ƙarshe da zai halarta.

Carney Chukwuemeka (Borussia Dortmund). An haifi Carney a birnin Ɓienna a Austria, kuma mahaifansa daga Nijeriya, ya fara buga wasa a matasan Ingila daga baya ya sauya zuwa buga wa babbar tawagar Austria wasa.

Switzerland:

Manuel Akanji (Manchester City) Tun farko Akanji ya samu damar wakiltar Switzerland ko kuma Nijeriya, an haife shi a birnin Wiesendangen garin mahaifiyarsa a Switzerland, mahaifinsa kuwa daga Nijeriya. Sai dai Switzerland yake yi wa wasa tun daga matasa har zuwa babbar tawagar ƙasar. Akanji yana daga cikin ginshiƙin masu tsaron bayan Manchester City, kuma yana taka muhimmiyar rawa a tawagarsa.

Noah Okafor (AC Milan), shima ɗanwasan an haife shi ne a birnin Binningen a Switzerland, wanda mahaifinsa daga Nijeriya yake. Ya fara buga wa babbar tawagar ta Switzerland wasa tun daga shekarar 2019.

Amurka:

Folarin Balogun (AS Monaco). Ɗan wasan ya samu damar wakiltar Amurka ko kuma Ingila, wanda aka haifa a birnin New York, amma a Ingila ya girma, iyayensa ƴan Nijeriya ne. Ya fara buga wa babbar tawagar Amurka wasa daga shekarar 2023.

Canada:

Tani Oluwaseyi (Minnesota United). Shima wannan ɗan wasan ya samu damar wakiltar Super Eagles ko kuma Canada. An haife shi a babban birnin tarayyar Nijeriya, Abuja, amma sai iyayensa suka koma Canada suka zauna a Mississauga a Ontario a lokacin da Tani yake da shekara 10 da haihuwa. Daga nan ya fara buga wa tawagar Canada wasa.

Promise Dabid (Union SaintGilloise). Tun farko Promise ya samu damar wakiltar ƙasashe biyu tsakanin Canada da Nijeriya. An haife shi a Brampton a Ontario, kuma iyayensa ƴan Nijeriya ne, har ma ya fara buga wa matasan Nijeriya wasa daga baya ya zabi Canada, wadda ta fara saka shi a wasan babbar tawagar a watan Fabrairun 2025.

Owen Goodman ( South Simcoe United). An haifi Goodman a Landan, Ingila, iyayensa sun koma Canada yana da shekara biyar da haihuwa, inda ya girma a Alliston, Ontario a Canada. Yana buga wasa a South Simcoe United, wanda tun farko mai tsaron baya ne, amma yanzu ya koma tsare raga. Mahaifinsa Philip ɗan Ingila ne, yayin da mahaifiyarsa Abi ƴar Ogbomosho ce a Nijeriya.

Afirka ta Kudu:

Ime Okon (SuperSport United) An haifi Ime a birnin Johannesburg a Afirka ta Kudu, inda mahaifinsa ne daga Nijeriya, kuma rayuwarsa gabaki ɗaya a Afirka ta Kudu ya yi ta, hakan ya sa ya zabi buga wa ƙasar wasa. Waɗannan ƴan wasa suna nuna yadda ƙwallon ƙafa ke zama wasan duniya, inda kenan babu wata iyaka ko katanga tsakanin ƙasashe.

Norway:

Antonio Eromonsele Nordby Nusa (RB Leipzig). An haifi ɗan ƙwallon ranar 17 ga watan Afirilun 2005 a Langhus, Norway, wanda ke buga wasa a RB Leipzig mai buga gasar Bundesliga ta Jamus. Mahaifinsa mutumin Benin ne a Nijeriya, yayin da mahaifiyarsa ƴar Norway ce.

Wannan lamari yana da muhimmanci sosai ga Nijeriya. Duk da cewa Super Eagles ba ta kai ga samun tikitin shiga gasar ba, Nijeriya na da tasiri a ƙwallon ƙafa ta hanyar ƴan asalin ƙasar da ke buga wasa a manyan ƙasashe a duniya.

Sannan hakan yana nuna abubuwa uku masu muhimmanci:

Ƙwarewa, Inganci da hazaƙar ƴan Nijeriya, Yawan ƴan wasa masu asali daga Nijeriya a manyan liglig a duniya, yana nuna irin baiwar da ƙasar nan ke da ita a fannin ƙwallon ƙafa.

Rashin tsarin riƙe ƴan wasa.  Wasu daga cikin waɗannan ƴanwasan sun zabi wakiltar wasu ƙasashe saboda tsarin horo da kulawa da suka samu a can.

Super Eagles
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Jiya Aka Fara Gasar Cin Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo
Super Eagles
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin
  • Sulaiman
    Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci
  • Sulaiman
    Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire
  • Sulaiman
    An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

MASU ALAKA

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya
Wasanni

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Lionel Messi: Mutum Ko Aljan
Wasanni

Lionel Messi: Mutum Ko Aljan

June 17, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasa 23 Da Eric Chelle Ya Gayyata Domin Buga Wasannin Sada Zumunci 

Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba

June 20, 2026
Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

Sakamakon Ziyartar Kasar Sin Sau 13 Shugaban Myanmar Na Da Mahanga Dangane Da Salon Zamanantarwa Irin Ta Sin

June 20, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Hijira: Malaman Musulunci Sun Buƙaci  Musulmi Su Yi Riƙo Da Gaskiya Da Adalci

June 20, 2026
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Rungumar Manufar Hadin Gwiwa Da Samun Ci Gaba Tare Da Kasar Sin A Fannin Kirkire-kirkire

June 20, 2026
Nijeriya

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

Sin Na Kira Ga Al’ummun Kasa Da Kasa Da Su Himmatu Wajen Tallafawa Ayyukan Jin kai

June 20, 2026
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Ceto Mutane 22 A Jihar Sakkwato

June 20, 2026
A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.