A bana ake cika shekaru 75 da ’yantar da jihar Xizang cikin lumana. Jihar wadda a kan kira da “Rumfar Duniya”, a yanzu ta sauya daga wani wuri kebabbe mai wahalar sha’ani zuwa sabon mafari na cimma damammakin zamanantarwa karkashin yanayin yanki mai kayatarwa, inda salon gwamnatin kasar Sin na jagorancin jihar ta Xizang ya zamo makullin cimma wannan nasara.
Wani binciken jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta gudanar ya nuna yadda kaso 74.8 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyi suka amince, cewa ci gaban tattalin arzikin Xizang, da yanayin ci gaban zamantakewar al’ummarsa ya samu gajiya daga salon zamanantarwa irin na Sin. Irin wannan yanayi na gwajin zamanantarwa, wanda a karkashinsa salon gargajiya ke hadewa da na zamani, kuma bil’adama da sauran halittu ke rayuwa tare cikin lumana, sun tabbatar da samun ci gaba a wannan yankin tsauni mai lullube da dusar kankara.Binciken na CGTN ya nuna yadda kaso 78.4 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyin suka amince, cewa tattalin arzikin Xizang ya samu ci gaban gaggawa.
Kana kaso 83 bisa dari sun jinjinawa nasarorin da jihar Xizang ta samu dangane da kare muhallin halittu da jagorancin aikin. Yanzu haka Xizang na ta lalubo hanyoyi marasa gurbata yanayi na sauya muhallin halittu mai ban sha’awa zuwa damar raya tattalin arziki, kuma jihar tana ci gaba da raba gudummawar Sin ta magance matsaloli ga aikin samar da ci gaba mai dorewa a muhallin halittun yankunan masu rauni dake sassan duniya. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post