Ma’aikatar kwashe shara ta Jihar Kano ƙarƙashin shugabancin MD Dakta Muhammad S. Khalil, ta ƙaddamar da shirin mai da shara taki domin samar da wadataccen taki ga manoman da nufin bunƙasa harkar noma da kuma tattalin arziƙi.
Shugaban REMASAB, MD Darkta Muhammad S. Khalil ya bayyana haka a lokacin ƙaddamar da wannan shiri wanda ya gudana a harabar ma’aikatar da ke Jihar Kano.
Ya ce wannan shiri ya samu kyakkyawan goyan bayane daga gwamnatin Jihar Kano bisa jagorancin, Injiniya Abba Kabir Yusuf da sauran hukumomi masu ruwa da tsaki. Ya ƙara da cewa abun a yaba ne ƙwarai da gaske ta yadda ƙungiyoyi da cibiyoyi suka ba da haɗin kai wajen haɗa hannu domin ba da kyakkyawar gudummawa ta ilimi da sauransu wajen ganin wannan aiki ya yi nasara a Kano.
Dakta Muhammad ya ce a wannan shiri an horar da mata kimanin 160, domin samun nasarar shirin wanda kuma yanzu haka sun mallaki katin cire kuɗin na ATM ta yadda za su iya cire kuɗinsu da hukumar za ta biya su a matsayin su da suka samu horo da kuma ci gaba da wannan aiki na mai da shara taki.
A ƙarshe, shugaban masu yin fakiti na ƙasa, Kwamired Salisu Ali Yarima, ya yaba wa gwamnatin Kano da ma’aikatar kula da mahalli ta Jihar Kano da kuma wannan hukuma ta REMASAB da ta samar da wannan babban al’amari da ake buƙatar.















Discussion about this post