ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

San Francisco Sabon Mafarin Hadin Gwiwar Sin Da Amurka Ne

by CGTN Hausa
3 years ago
Francisco

Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden, sun yi musayar ra’ayoyi mai zurfi, a rukunin gidajen alfarma na Filoli dake birnin San Francisco na kasar Amurka ranar Laraba. Taron kolin da aka dade ana jira, na zuwa ne shekara guda bayan ganawar shugabannin biyu a tsibirin Bali na kasar Indonesia.

A jawabinsa yayin ganawar shugaba Xi ya jaddada cewa, kasar Sin ta dukufa wajen samun daidaito, da dorewar dangantakar lumana da kasar Amurka. A lokaci guda kuma, kasar Sin tana da moriya da ka’idojin da suka kamata a kiyaye, da jan layin da ba za a iya ketarewa ba.

  • San Francisco Sabon Mafarin Hadin Gwiwar Sin Da Amurka Ne
  • Ka Hakura Da Zuwa Kotun Koli, Ka Jira 2027 – Musa Iliyasu Ga Abba

Kasar Sin na fatan kasashen biyu za su kasance abokan hulda masu mutunta juna da zaman tare cikin lumana. Taron dai ya kasance wani muhimmin zabi mai muhimmanci ga kasar Sin, don daidaita dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma halin da ake ciki a duniya.

ADVERTISEMENT

Masanin tattalin arziki na kasar Amurka Jeffrey Sachs ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, ra’ayin mutunta juna, da yin hadin gwiwa,da tattaunawa, da warware matsaloli tare, akwai “hikima sosai”, a cikinsa kuma yana da matukar muhimmanci.

Yana mai cewa, hadin gwiwar Sin da Amurka ba wai kawai kan muradun bai daya ne na kasashen biyu ba, yana kuma nuni da wani nauyi da ya rataya a wuyan kasashen duniya. A yayin taron, shugaba Xi ya yi kira ga kasashen biyu, da su hada kai a matsayinsu na manyan kasashe, yana mai jaddada cewa, za a iya magance matsalolin da ke addabar bil-Adama ne kawai ta hanyar hadin gwiwa tsakanin manyan kasashe.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Yarjejeniyar da aka cimma a yayin taron na San Francisco, ta nuna cewa, kasashen biyu suna da moriyar bai daya, kuma za su iya yin hadin gwiwa don samun sakamako mai tarin yawa. Dangantakar Sin da Amurka mai dorewa ba tunanin fata ba ne. Don haka, ya bukaci kasashen biyu su yi aiki tare. Kuma tattaunawa shi ne mataki na farko na amincewa da juna, da mutunta juna da kuma hada kai. Daga Bali zuwa San Francisco, babban jirgin ruwa na hadin gwiwar kasashen Sin da Amurka, ya yi tattaki ta cikin duwatsun teku da kadawar igiyar ruwa. Amma ba a San Francisco za a tsaya ba.

Birnin, wanda ya shaida tarihin musanya tsakanin Sinawa da Amurkawa na tsawon karni, wani sabon mafari ne na dangantakar kasashen Sin da Amurka. (Ibrahim)

Francisco
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Zargin Yaudara: Wani Tela Ya Kashe Tsohuwar Masoyiyarsa A Kaduna

'Yansanda Sun Cafke Malamin Addini Da Sassan Mutum Danye A Oyo

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.