Mai Martaba Sarkin Katagum, Dakta Umar Faruk Umar Kabir, ya jagoranci addu’ar roƙon ruwa da aka gudanar a garin Azare, hedikwatar Masarautar Katagum, sakamakon ƙarancin ruwan sama da ake fuskanta a yankin a bana, lamarin da ya haifar da damuwa ga manoma da sauran al’umma.
An gudanar da addu’ar ne a ranar Laraba, 22 ga Yuli, 2026, a Filin Masallacin Idi na Azare da ke kusa da makabartar garin. Dubban al’umma ne suka hallara domin neman taimakon Allah Maɗaukakin Sarki Ya saukar da ruwan sama mai albarka da zai amfani ƙasa da jama’a.
Taron ya samu halartar manyan malamai, hakimai, masu unguwanni, shugabannin al’umma da ɗimbin jama’a daga Azare da maƙwabtanta. Mahalarta taron sun haɗu cikin tawali’u da ƙanƙan da kai wajen roƙon Allah Ya kawo ƙarshen ƙarancin ruwan saman da ake fuskanta.
Babban Limamin Masallacin Juma’a na Kofar Fada da ke Azare, Alaramma Malam Ayuba, shi ne ya jagoranci addu’o’in. Ya roƙi Allah Subhanahu wa Ta’ala Ya saukar da ruwan sama mai amfani da albarka, ya yalwata amfanin gona, ya kare al’umma daga fari, yunwa da sauran ƙalubalen rayuwa.
Haka kuma ya yi addu’ar Allah Ya tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da kwanciyar hankali a Azare, Jihar Bauchi da Nijeriya baki ɗaya, tare da bai wa shugabanni hikima da adalci wajen gudanar da al’amuran jama’a.
Bayan kammala addu’ar, an yi kira ga al’umma da su ci gaba da yawaita addu’a, istigfari da tuba, tare da kyautata mu’amala da juna, kasancewar waɗannan na daga cikin hanyoyin neman rahamar Allah da saukar ni’imominsa.
Mahalarta taron sun bayyana fatan cewa Allah Maɗaukakin Sarki zai karɓi addu’o’insu, ya saukar da ruwan sama mai albarka wanda zai amfani manoma, makiyaya da daukacin al’umma, tare da sanya albarka a cikin amfanin gona da rayuwar jama’a.














