ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

by Sulaiman
2 hours ago
Roƙon Ruwa

Mai Martaba Sarkin Katagum, Dakta Umar Faruk Umar Kabir, ya jagoranci addu’ar roƙon ruwa da aka gudanar a garin Azare, hedikwatar Masarautar Katagum, sakamakon ƙarancin ruwan sama da ake fuskanta a yankin a bana, lamarin da ya haifar da damuwa ga manoma da sauran al’umma.

An gudanar da addu’ar ne a ranar Laraba, 22 ga Yuli, 2026, a Filin Masallacin Idi na Azare da ke kusa da makabartar garin. Dubban al’umma ne suka hallara domin neman taimakon Allah Maɗaukakin Sarki Ya saukar da ruwan sama mai albarka da zai amfani ƙasa da jama’a.

Taron ya samu halartar manyan malamai, hakimai, masu unguwanni, shugabannin al’umma da ɗimbin jama’a daga Azare da maƙwabtanta. Mahalarta taron sun haɗu cikin tawali’u da ƙanƙan da kai wajen roƙon Allah Ya kawo ƙarshen ƙarancin ruwan saman da ake fuskanta.

ADVERTISEMENT

Babban Limamin Masallacin Juma’a na Kofar Fada da ke Azare, Alaramma Malam Ayuba, shi ne ya jagoranci addu’o’in. Ya roƙi Allah Subhanahu wa Ta’ala Ya saukar da ruwan sama mai amfani da albarka, ya yalwata amfanin gona, ya kare al’umma daga fari, yunwa da sauran ƙalubalen rayuwa.

Haka kuma ya yi addu’ar Allah Ya tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da kwanciyar hankali a Azare, Jihar Bauchi da Nijeriya baki ɗaya, tare da bai wa shugabanni hikima da adalci wajen gudanar da al’amuran jama’a.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

Bayan kammala addu’ar, an yi kira ga al’umma da su ci gaba da yawaita addu’a, istigfari da tuba, tare da kyautata mu’amala da juna, kasancewar waɗannan na daga cikin hanyoyin neman rahamar Allah da saukar ni’imominsa.

Mahalarta taron sun bayyana fatan cewa Allah Maɗaukakin Sarki zai karɓi addu’o’insu, ya saukar da ruwan sama mai albarka wanda zai amfani manoma, makiyaya da daukacin al’umma, tare da sanya albarka a cikin amfanin gona da rayuwar jama’a.

Roƙon Ruwa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?
  • Sulaiman
    Gwamnan Nasarawa Ya Sallami Kwamishinoni Shida Na Majalisar Zartarwar Jihar
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar
Labarai

Gwamnan Nasarawa Ya Sallami Kwamishinoni Shida Na Majalisar Zartarwar Jihar

July 23, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

'Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

July 23, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar

Gwamnan Nasarawa Ya Sallami Kwamishinoni Shida Na Majalisar Zartarwar Jihar

July 23, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Akpabio

Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

July 23, 2026
Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

July 22, 2026
Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

July 22, 2026
An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

July 22, 2026
Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

July 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.