Biyo bayan karancin takardar kudin Naira, wasu almajirai a jihar Jigawa sun koka kan raguwar samun kudin sadaka.
Wasu daga cikin almajiran sun bayyana damuwarsu a lokacin da suke zantawa da Daily Post a Dutse babban birnin jihar.
Malam Sani, daya daga cikin almajiran da ke kan hanyar Kiyawa a Dutse, ya ce kafin gabatar da wannan sabon kudirin, ya kan samu isassun kudade da za su biya masa bukatunsa da na iyalansa.
Malama Halima, daya daga cikin matan da ke bara a kan hanyar Kiyawa a Dutse, ta koka da yadda a yanzu take fuskantar wahalar ciyar da kanta da ‘ya’yanta guda biyu.
“Tun da safe da muka fito, Naira 70 kawai na samu kuma dole in nemo abinda zan ciyar da kaina da yara na,” inji ta.
Sai dai, mabaratan sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta duba lamarin domin rage wa talakawa radadin da suke ciki.