Cibiyar Ƙwararrun Masana Lissafin Kuɗi ta Nijeriya (ICAN) rehen Jihar Kano ta bayyana ƙudirinta na tallafa wa al’ummar Kano a fannin akanta da samun aiki cikin sauki, domin tabbatar da an cika buƙatunsu tare da tabbatar da jin daɗin mambobinta.
Shugaban cibiyar ICAN resnen Jihar Kano, Alhaji Jamilu Abdullahi Ɗaihur ne ya bayyana haka a wata ganawa da manema labarai.Alhaji Ɗaihur ya ce ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen da cibiyar ke fuskanta a yanzu shi ne, rashin ofis nasu na dindindin, domin wajen da suke amfani da shi yanzu na wucin-gadi ne, Gwamnatin Jihar Kano ce ta ba su aro a ginin ɗakin karatu na Murtala Muhammad.
Ya ce wani ƙalubalen da ke damun su shi ne, na rashin sha’awar al’ummar Kano wajen shiga ICAN, wanda kuma an kawo shi Jihar Kano ne don ya amfanar da al’ummarta.
Ya yi kira ga al’ummar Kano su zo su shiga ICAN domin samun cin gajiyar amfani da take da shi sosai wanda gwamnati da al’umma za su amfana.Shugaban ICAN reshen Jihar Kano, Alhaji Ɗaihur ya bayyana cewa tsarin shiga cibiyar an sauƙaƙa shi ga waɗanda suke matakin farko suna ba su laccoci kyauta, suna taimakawa wajen biya musu kuɗin jarrabawa.
Ya bayyana matakan shiga cibiyar cewa, dole ne mutum ya kasance yana da takardar shaidar WAEC ko NECO da a ƙalla ‘credit 5’ ciki har da lissafi da Turanc ga waɗanda suka kamala karatun sakandire.Sannan ya ce matakin shaidar digiri ko HND za a yi masa rajista kai tsaye, ba lallai sai yana da shaidar yin karatun fannin tattalin arziƙi ba, kowane fanni ma za a karɓa.
Ya yi nuni da cewa duk da yawan al’ummar Kano da ƴan kasuwarsu har yanzu akwai ƙarancin ƙwararrun masana akanta, wannan ne ya sa suke yunƙurin wayar da kan jama’asu wajen shiga ɓangare daban-dabn.
Alhaji Ɗaihur ya ce reshen cibiyar ICAN a Jihar Kano za ta ci gaba da wayar da kan jama’a domin samar da ƙwararrun akantoci da za su taimaka wajen bunƙasa tattalin arziƙin jihar.













