Majalisar sarakunan Jihar Zamfara, ƙarƙashin jagorancin Sarkin Zamfara, Alhaji Attahiru Ahmad ta sanya takalmin ƙarfe ga duk wanda ke hura wutar rikicin siyasa a jihar.
Shugaban majalisar sarakunan, Alhaji Attahiru ya bayyana haka ne jim kaɗan bayan tattaunawar sirri da suka yi da Gwamna jihar, Dauda Lawal a gidan gwamnati da ke Gusau.
Alhaji Attahiru ya bayyana cewa, wakilan sarakunan sun yi tattaki zuwa Abuja da Kaduna domin ganawa da Sanata Abdul’aziz Yari da ministan tsaro, Bello Matawalen Maradun, domin sasantasu kan saɓanin da suke ganin sun samu, wanda ya jawo magoya bayansu na ta cacar baki da sukar juna a kafafen sada zumunta.
Mai Martaba Attahiru ya nuna takaicinsa kan yadda ake fito na fito tsakanin mabiya ƴaniyasa babu ƙaƙƙautawa.Ya ce wannan ne ya sa suka kai ziyara tsakanin Sanata Abdul’aziz Yari da Bello Matawalle kan duk wani mabiyansu da ke ɓatanci ga wani lallai zai gamu da hukunci mai tsanani daga hukuma.
A cewarsa, duk wanda ya ƙi ji, to lallai ba zai ƙi gani ba.Haka kuma ya ce sun umarci duk wani uban ƙasa da su sanya idanu kan masu san tada fitina a tsakanin al’umma ko wane ne zai gamu da mumanan hukunci.
A ƙarshe, Sarki Attahiru ya yi kira ga tsaffin gwamnoni da mayan ƴaniyasa da su haɗa kawunansu wajen kawo ayyukan ci gaban Jihar Zamfara da kuma samar da tsaro a faɗin jihar baki ɗaya.













