Sani Abdullahi Shinkafi, mai neman takarar Sanatan Zamfara ta Arewa, ya maka Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da jam’iyyar APC a kotun tarayya da ke Gusau kan zargin tafka kura-kurai a zaben fidda gwani na sanatoci na APC da aka kammala kwanan nan.
Lauya Garba Galadi ne ya bayyana hakan ga manema labarai jim kadan bayan shigar da karar a madadin wanda yake karewa a kotun tarayya da ke Gusau.
A cewar Galadi, Shinkafi ya garzaya kotu ne saboda abin da ya bayyana a matsayin rashin bin dokar zabe da kuma ka’idoji da dokokin da ke jagorantar gudanar da zabukan fidda gwani na jam’iyyu suka tanadar.
ADVERTISEMENT















Discussion about this post