Jam’iyyar APC a Jihar Kebbi ta dakatar da shugabanta na jiha, Abubakar Kana-Zuru, da kuma shugaban jam’iyyar na ƙaramar hukumar Zuru, Aliyu Abiola, kan yadda suka tafiyar da zaɓen cike gurbi na mazaɓar Zuru da aka gudanar a ƙarshen makon da ya gabata.
A wata sanarwa da sakataren jam’iyyar na jiha, Sa’idu Muhammad Kimba, ya fitar, APC ta ce an zargi jami’an da gazawa wajen tara magoya baya, rashin hulɗa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar da kuma ƙin bin wasu ƙa’idojin jam’iyyar.
Jam’iyyar ta ce binciken da ta gudanar ya tabbatar da zarge-zargen, lamarin da ya sa aka ɗauki matakin dakatar da su.
An kuma umarci mataimakin shugaban APC na jihar ya jagoranci jam’iyyar na riƙo har zuwa wani lokaci.
A wani mataki makamancin haka, Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya dakatar da Kwamishinan Inganta Kiwo, Kabir Zuru.
An umarci kwamishinan da ya miƙa duk wasu ayyuka da kadarorin gwamnati da ke hannunsa ga sakataren ma’aikatar har zuwa wani lokaci.
Masu sarhi kan harkokin siyasa na ganin cewa dakatarwar na da alaƙa da zaɓen cike gurbi na Zuru, wanda ya samu ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a.
Duk da APC ta lashe zaɓen, mutum kusan 5,000 ne kawai suka kaɗa ƙuri’a daga cikin sama da mutum 109,000 da suka yi rajista.














