ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Na Kasar Sin: Da Sanyin Safiya Ake Kama Fara

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Sin

Shekarar 2026 ita ce ta fara aiwatar da shirin bunkasa tattalin arzikin kasa da zamantakewar al’umma karo na 15 na kasar Sin, kuma a yayin da tuni shirye-shirye na amincewa da daftarin shirin suka kai kusan matakin karshe, yankuna daban-daban na kasar sun dau harama kan ayyukan da za su aiwatar.

Amma da yake a bara, kasar Sin ta yi nasarar hawa mizanin manyan kasashe 10 mafiya fasahar kirkire-kirkire a duniya, abin da ya fi ba ni sha’awa shi ne kokarin da ake yi na tsare-tsaren cikin gida a bangaren ci gaba da raya kimiyya da fasaha a karkashin shirin na shekaru biyar-biyar, kasancewar a yanzu a duniya, babu bangare da ake gogoriyon zuba gasa kamar na ci gaban fasaha. Dama tuni, a shekarar 2025, hukumomin gwamnatoci sun yi amfani da dabarun gudanar da gasa a bangaren binciken kimiyya domin kara kuzarin bunkasar sashen, kana suka dauki matakan magance kalubalen kudi ga kanana da matsakaitan kamfanonin fasaha ta hanyar samar da lamuni na ayyukan fasaha da kuma lamuni na fara kasuwancin kayayyakin fasaha da aka kera.

Kasancewar da sanyin safiya ake kama fara, tun a farko-farkon 2026, gwamnatocin kananan hukumomi, da larduna masu cin gashin kansu sun gudanar da manyan tarurrukansu na farko a wannan shekarar domin kara kimtsa wa shirin na shekaru biyar-biyar karo na 15. Daga manyan shawarwarin da aka gabatar a tarurrukan, wadanda aka fi ba su karfi su ne batun sabbin kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da kuma dabarun da za su taimaka wajen daidaita shirye-shiryen gwamnatocin yankuna da na gwamnatin tsakiya da zimmar samun tsararrun hanyoyin samun bunkasa.

ADVERTISEMENT

Daga abubuwan da wasu larduna da yankuna suka kuduri aniyar cimmawa a karkashin shirin karo na 15, akwai daga darajar tsoffin sassansu na ci gaba ta hanyar sanya musu fasahohin zamani da kuma amfani da makamashi mara gurbata muhalli. Misali, lardin Shanxi zai hade bangaren sabbin kirkire-kirkiren fasaha da na daga darajar masana’antu domin samar da sahihin tsarin masana’antu na zamani bisa amfani da albarkatun da yankin ya fi karfi a kai. Lardin Heilongjiang ya sha damarar kawo sauyi na habaka bangaren albarkatunsa na kankara ta yadda zai zama ingantaccen tattalin arziki mai amfani da fasaha. Yayin da kuma Guangdong ya kuduri aniyar ci gaba da shigar da amfani da fasahar kirkirarriyar basira wajen gudanar da ayyukan kamfanoni. Duka wadanan kadan ne daga sauran dimbin shirye-shiryen da ake yi a cikin gida domin cimma burin zamanantar da kasar Sin yadda ya kamata.

Akwai darussa da dama da kasashenmu na Afirka za su dauka daga irin wannan shiri a kan lokaci da kuma sanya ido wajen ganin an yi abin da ya kamata a lokacin da ya dace, musamman a halin yanzu da suke shirin fara aiwatar da kasafin kudi na shekarar 2026. Kasashen su yi kokarin gyara ginshikai masu muhimmanci na amfani da fasaha kamar bangaren makamashi da sadarwa, ta yadda za a samu sakamakon da ake bukata, kuma abu mafi muhimmanci shi ne yin aiki a kan lokaci, domin da sanyin safiya ake kama fara, ba da rana ba, idan aka bari rana ta daga watsewa suke yi! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

LABARAI MASU NASABA

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Taya Kim Jong-Un Murnar Cika Shekaru 78 Da Kafuwar Koriya Ta Arewa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
  • Sulaiman
    Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

MASU ALAKA

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Next Post
Tinubu, Shettima Zasu Ziyarci Kano Halartar Tarɓar Gwamna Yusuf Zuwa APC

Tinubu, Shettima Zasu Ziyarci Kano Halartar Tarɓar Gwamna Yusuf Zuwa APC

LABARAI MASU NASABA

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Sin

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Sin

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.