ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Na Kasar Sin: Da Sanyin Safiya Ake Kama Fara

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Sin

Shekarar 2026 ita ce ta fara aiwatar da shirin bunkasa tattalin arzikin kasa da zamantakewar al’umma karo na 15 na kasar Sin, kuma a yayin da tuni shirye-shirye na amincewa da daftarin shirin suka kai kusan matakin karshe, yankuna daban-daban na kasar sun dau harama kan ayyukan da za su aiwatar.

Amma da yake a bara, kasar Sin ta yi nasarar hawa mizanin manyan kasashe 10 mafiya fasahar kirkire-kirkire a duniya, abin da ya fi ba ni sha’awa shi ne kokarin da ake yi na tsare-tsaren cikin gida a bangaren ci gaba da raya kimiyya da fasaha a karkashin shirin na shekaru biyar-biyar, kasancewar a yanzu a duniya, babu bangare da ake gogoriyon zuba gasa kamar na ci gaban fasaha. Dama tuni, a shekarar 2025, hukumomin gwamnatoci sun yi amfani da dabarun gudanar da gasa a bangaren binciken kimiyya domin kara kuzarin bunkasar sashen, kana suka dauki matakan magance kalubalen kudi ga kanana da matsakaitan kamfanonin fasaha ta hanyar samar da lamuni na ayyukan fasaha da kuma lamuni na fara kasuwancin kayayyakin fasaha da aka kera.

Kasancewar da sanyin safiya ake kama fara, tun a farko-farkon 2026, gwamnatocin kananan hukumomi, da larduna masu cin gashin kansu sun gudanar da manyan tarurrukansu na farko a wannan shekarar domin kara kimtsa wa shirin na shekaru biyar-biyar karo na 15. Daga manyan shawarwarin da aka gabatar a tarurrukan, wadanda aka fi ba su karfi su ne batun sabbin kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da kuma dabarun da za su taimaka wajen daidaita shirye-shiryen gwamnatocin yankuna da na gwamnatin tsakiya da zimmar samun tsararrun hanyoyin samun bunkasa.

ADVERTISEMENT

Daga abubuwan da wasu larduna da yankuna suka kuduri aniyar cimmawa a karkashin shirin karo na 15, akwai daga darajar tsoffin sassansu na ci gaba ta hanyar sanya musu fasahohin zamani da kuma amfani da makamashi mara gurbata muhalli. Misali, lardin Shanxi zai hade bangaren sabbin kirkire-kirkiren fasaha da na daga darajar masana’antu domin samar da sahihin tsarin masana’antu na zamani bisa amfani da albarkatun da yankin ya fi karfi a kai. Lardin Heilongjiang ya sha damarar kawo sauyi na habaka bangaren albarkatunsa na kankara ta yadda zai zama ingantaccen tattalin arziki mai amfani da fasaha. Yayin da kuma Guangdong ya kuduri aniyar ci gaba da shigar da amfani da fasahar kirkirarriyar basira wajen gudanar da ayyukan kamfanoni. Duka wadanan kadan ne daga sauran dimbin shirye-shiryen da ake yi a cikin gida domin cimma burin zamanantar da kasar Sin yadda ya kamata.

Akwai darussa da dama da kasashenmu na Afirka za su dauka daga irin wannan shiri a kan lokaci da kuma sanya ido wajen ganin an yi abin da ya kamata a lokacin da ya dace, musamman a halin yanzu da suke shirin fara aiwatar da kasafin kudi na shekarar 2026. Kasashen su yi kokarin gyara ginshikai masu muhimmanci na amfani da fasaha kamar bangaren makamashi da sadarwa, ta yadda za a samu sakamakon da ake bukata, kuma abu mafi muhimmanci shi ne yin aiki a kan lokaci, domin da sanyin safiya ake kama fara, ba da rana ba, idan aka bari rana ta daga watsewa suke yi! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Tinubu, Shettima Zasu Ziyarci Kano Halartar Tarɓar Gwamna Yusuf Zuwa APC

Tinubu, Shettima Zasu Ziyarci Kano Halartar Tarɓar Gwamna Yusuf Zuwa APC

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.