ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15 Na Kasar Sin: Da Sanyin Safiya Ake Kama Fara

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Sin

Shekarar 2026 ita ce ta fara aiwatar da shirin bunkasa tattalin arzikin kasa da zamantakewar al’umma karo na 15 na kasar Sin, kuma a yayin da tuni shirye-shirye na amincewa da daftarin shirin suka kai kusan matakin karshe, yankuna daban-daban na kasar sun dau harama kan ayyukan da za su aiwatar.

Amma da yake a bara, kasar Sin ta yi nasarar hawa mizanin manyan kasashe 10 mafiya fasahar kirkire-kirkire a duniya, abin da ya fi ba ni sha’awa shi ne kokarin da ake yi na tsare-tsaren cikin gida a bangaren ci gaba da raya kimiyya da fasaha a karkashin shirin na shekaru biyar-biyar, kasancewar a yanzu a duniya, babu bangare da ake gogoriyon zuba gasa kamar na ci gaban fasaha. Dama tuni, a shekarar 2025, hukumomin gwamnatoci sun yi amfani da dabarun gudanar da gasa a bangaren binciken kimiyya domin kara kuzarin bunkasar sashen, kana suka dauki matakan magance kalubalen kudi ga kanana da matsakaitan kamfanonin fasaha ta hanyar samar da lamuni na ayyukan fasaha da kuma lamuni na fara kasuwancin kayayyakin fasaha da aka kera.

Kasancewar da sanyin safiya ake kama fara, tun a farko-farkon 2026, gwamnatocin kananan hukumomi, da larduna masu cin gashin kansu sun gudanar da manyan tarurrukansu na farko a wannan shekarar domin kara kimtsa wa shirin na shekaru biyar-biyar karo na 15. Daga manyan shawarwarin da aka gabatar a tarurrukan, wadanda aka fi ba su karfi su ne batun sabbin kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da kuma dabarun da za su taimaka wajen daidaita shirye-shiryen gwamnatocin yankuna da na gwamnatin tsakiya da zimmar samun tsararrun hanyoyin samun bunkasa.

ADVERTISEMENT

Daga abubuwan da wasu larduna da yankuna suka kuduri aniyar cimmawa a karkashin shirin karo na 15, akwai daga darajar tsoffin sassansu na ci gaba ta hanyar sanya musu fasahohin zamani da kuma amfani da makamashi mara gurbata muhalli. Misali, lardin Shanxi zai hade bangaren sabbin kirkire-kirkiren fasaha da na daga darajar masana’antu domin samar da sahihin tsarin masana’antu na zamani bisa amfani da albarkatun da yankin ya fi karfi a kai. Lardin Heilongjiang ya sha damarar kawo sauyi na habaka bangaren albarkatunsa na kankara ta yadda zai zama ingantaccen tattalin arziki mai amfani da fasaha. Yayin da kuma Guangdong ya kuduri aniyar ci gaba da shigar da amfani da fasahar kirkirarriyar basira wajen gudanar da ayyukan kamfanoni. Duka wadanan kadan ne daga sauran dimbin shirye-shiryen da ake yi a cikin gida domin cimma burin zamanantar da kasar Sin yadda ya kamata.

Akwai darussa da dama da kasashenmu na Afirka za su dauka daga irin wannan shiri a kan lokaci da kuma sanya ido wajen ganin an yi abin da ya kamata a lokacin da ya dace, musamman a halin yanzu da suke shirin fara aiwatar da kasafin kudi na shekarar 2026. Kasashen su yi kokarin gyara ginshikai masu muhimmanci na amfani da fasaha kamar bangaren makamashi da sadarwa, ta yadda za a samu sakamakon da ake bukata, kuma abu mafi muhimmanci shi ne yin aiki a kan lokaci, domin da sanyin safiya ake kama fara, ba da rana ba, idan aka bari rana ta daga watsewa suke yi! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Tinubu, Shettima Zasu Ziyarci Kano Halartar Tarɓar Gwamna Yusuf Zuwa APC

Tinubu, Shettima Zasu Ziyarci Kano Halartar Tarɓar Gwamna Yusuf Zuwa APC

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.