A yau Litinin shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira ga daukacin kasashen duniya da su martaba hanyoyin neman ci gaba da al’ummun mabanbantan kasashe suka zabawa kan su, su kuma rungumi dalilan kafuwa, da ka’idojin gudanar da yarjejeniyar kafa MDD. Shugaba Xi ya bukaci manyan kasashen duniya da su wuce gaba wajen ganin an cimma wannan manufa.
Shugaban na Sin wanda ya yi tsokacin a birnin Beijing, yayin zantawarsa da firaministan Ireland Micheal Martin wanda ke ziyarar aiki a kasar Sin, ya ce a wannan duniya mai fama da sauye-sauye da hargitsi, daukar matakan kashin kai da cin zali na matukar gurgunta odar kasa da kasa. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)














Discussion about this post