Bisa gayyatar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi masa, shugaban Amurka Donald Trump, zai gudanar da ziyarar aiki a kasar Sin tsakanin ranakun Laraba zuwa Juma’a, kamar dai yadda kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin ya bayyana a Litinin din nan.
A wani ci gaban kuma, ma’aikatar cinikayya ta Sin ta ce bisa amincewar kasashen biyu, mataimakin firaministan kasar Sin He Lifeng, zai jagoranci wata tawaga zuwa koriya ta kudu, domin gudanar da tattaunawar tattalin arziki da cinikayya tare da tawagar Amurka daga gobe Talata zuwa jibi Laraba.
Sassan biyu za su tattauna bisa la’akari da muhimman kudurorin da shugabannin kasashen biyu suka amincewa yayin ganawarsu a Busan, da sauran tattaunawa da suka yi a baya, kana za su gudanar da shawarwari dangane da batutuwan tattalin arziki da cinikayya dake jan hankulan kasashen biyu.















Discussion about this post